• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka, Kasar Da Ke Kawo Cikas Ga Kokarin Duniya Na Shawo Kan Annobar Covid-19

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka, Kasar Da Ke Kawo Cikas Ga Kokarin Duniya Na Shawo Kan Annobar Covid-19
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Annobar Covid-19 matsala ce da ke addabar duniya baki daya, wadda ke bukatar hadin gwiwar kasa da kasa don shawo kanta. Sai dai abin takaici shi ne, cikin shekaru uku da suka wuce, kasancewarta babbar kasa mafi karfi a duniya, Amurka ta yi ta kawo cikas ga kokarin kasa da kasa na shawo kan cutar, a maimakon daukar nauyin da ke rataye a wuyanta.

A matsayinta na kasa mai ci gaban aikin kiwon lafiya a duniya, mahukuntan kasar ta Amurka ba su dauki matakan da suka kamata ba na tinkarar annobar, inda suka yi biris da lafiyar al’umma da rayukansu, kuma a maimakon haka, sai suka mai da hankali a kan siyasantar da annobar, matakin da ya sabbaba saurin yaduwar annobar.

  • Shugaba Talon Na Benin Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin

A cikin shekarun uku da suka wuce, an samu yaduwar kusan dukkanin nau’o’in cutar Covid-19 a kasar, inda sama da ’yan kasar miliyan 100 suka harbu da cutar, baya ga kuma sama da miliyan daya da suka rasa rayukansu. Ban da haka, gwamnatin kasar ba ta dauki mataki na kayyade harkokin fita daga kasar ba, inda ta bar cutar ta rika yaduwa zuwa sauran sassan duniya.

Alkaluman da aka samar sun yi nuni da cewa, daga watan Afrilun shekarar 2020 zuwa watan Maris na shekarar 2021, gaba daya al’ummar kasar miliyan 23 da dubu 195 suka fice daga kasar, wadanda suka tafi sassa daban daban na duniya. Sa’an nan, yadda kasar ta tilastawa bakin haure da su koma kasashensu na asali ba tare da lura da yanayin lafiyarsu ba, ya kara tsananta yanayin annobar da kasashen Latin Amurka ke ciki.

A yayin da duniya ke kokarin shawo kan annobar, kasar Amurka ta kuma fice daga hukumar lafiya, baya ga tara dimbin rigakafin cutar a gida, ba tare da raba su ga sauran kasashe masu bukata ba. Alkaluman da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Amurka ta samar sun shaida cewa, daga watan Maris zuwa watan Satumban shekarar 2021, Amurkar ta bata a kalla rigakafi miliyan 15.1. Idan ba a manta ba, Amurka ta tura rigakafin da lokacin aikinsa ya kusan karewa zuwa kasashen Afirka, matakin da ya jawo suka daga kasashen.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

In mun waiwayi tarihi, sau tari mabambantan annoba sun haifar da munanan hasarori ga ’yan Adam, kuma tarihi ya shaida cewa, cuta ba ta san iyaka ko kabila ba. Shekaru ukun da suka wuce da ake yaki da cutar Covid-19 ma sun shaida mana cewa, ’yan Adam makomarsu daya ce, kuma siyasantar da annobar ba zai haifar da komai ba illa lalata hadin gwiwar kasa da kasa wajen dakile cutar, tare da haifar da karin hasarori ga al’ummar duniya. (Mai Zane: Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Wadda Ta Fi Yada Cutar COVID-19 Ta Bayyana Alkalumanta Kan Yanayin Yaduwar Cutar

Next Post

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Neja, Sun Kwace Makamai

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

16 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

18 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

18 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

22 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

24 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Neja, Sun Kwace Makamai

'Yansanda Sun Kashe 'Yan Bindiga 4 A Neja, Sun Kwace Makamai

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.