ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka, Kasar Da Ke Kawo Cikas Ga Kokarin Duniya Na Shawo Kan Annobar Covid-19

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Annobar Covid-19 matsala ce da ke addabar duniya baki daya, wadda ke bukatar hadin gwiwar kasa da kasa don shawo kanta. Sai dai abin takaici shi ne, cikin shekaru uku da suka wuce, kasancewarta babbar kasa mafi karfi a duniya, Amurka ta yi ta kawo cikas ga kokarin kasa da kasa na shawo kan cutar, a maimakon daukar nauyin da ke rataye a wuyanta.

A matsayinta na kasa mai ci gaban aikin kiwon lafiya a duniya, mahukuntan kasar ta Amurka ba su dauki matakan da suka kamata ba na tinkarar annobar, inda suka yi biris da lafiyar al’umma da rayukansu, kuma a maimakon haka, sai suka mai da hankali a kan siyasantar da annobar, matakin da ya sabbaba saurin yaduwar annobar.

  • Shugaba Talon Na Benin Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin

A cikin shekarun uku da suka wuce, an samu yaduwar kusan dukkanin nau’o’in cutar Covid-19 a kasar, inda sama da ’yan kasar miliyan 100 suka harbu da cutar, baya ga kuma sama da miliyan daya da suka rasa rayukansu. Ban da haka, gwamnatin kasar ba ta dauki mataki na kayyade harkokin fita daga kasar ba, inda ta bar cutar ta rika yaduwa zuwa sauran sassan duniya.

ADVERTISEMENT

Alkaluman da aka samar sun yi nuni da cewa, daga watan Afrilun shekarar 2020 zuwa watan Maris na shekarar 2021, gaba daya al’ummar kasar miliyan 23 da dubu 195 suka fice daga kasar, wadanda suka tafi sassa daban daban na duniya. Sa’an nan, yadda kasar ta tilastawa bakin haure da su koma kasashensu na asali ba tare da lura da yanayin lafiyarsu ba, ya kara tsananta yanayin annobar da kasashen Latin Amurka ke ciki.

A yayin da duniya ke kokarin shawo kan annobar, kasar Amurka ta kuma fice daga hukumar lafiya, baya ga tara dimbin rigakafin cutar a gida, ba tare da raba su ga sauran kasashe masu bukata ba. Alkaluman da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Amurka ta samar sun shaida cewa, daga watan Maris zuwa watan Satumban shekarar 2021, Amurkar ta bata a kalla rigakafi miliyan 15.1. Idan ba a manta ba, Amurka ta tura rigakafin da lokacin aikinsa ya kusan karewa zuwa kasashen Afirka, matakin da ya jawo suka daga kasashen.

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

In mun waiwayi tarihi, sau tari mabambantan annoba sun haifar da munanan hasarori ga ’yan Adam, kuma tarihi ya shaida cewa, cuta ba ta san iyaka ko kabila ba. Shekaru ukun da suka wuce da ake yaki da cutar Covid-19 ma sun shaida mana cewa, ’yan Adam makomarsu daya ce, kuma siyasantar da annobar ba zai haifar da komai ba illa lalata hadin gwiwar kasa da kasa wajen dakile cutar, tare da haifar da karin hasarori ga al’ummar duniya. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
Daga Birnin Sin

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 4 A Neja, Sun Kwace Makamai

'Yansanda Sun Kashe 'Yan Bindiga 4 A Neja, Sun Kwace Makamai

LABARAI MASU NASABA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.