ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

by Sulaiman
7 months ago
Kotu

Masu karatu barkanmu da war haka. Yau Alƙalaminmu karkata ya yi zuwa wani ɓangare mai mahimmanci a rayuwar ‘yan ƙasa, wanda idan ya faɗi ko ya samu tangarɗa, rayuwar masu rauni, da masu ƙaramin ƙarfi musamman mafi yawancin ‘yan ƙasa, tana cikin barazana.

 

Wannann ɓangare, shi ne gatan talaka, gatan wanda aka danne ko aka tauye wa hakki, wato ɓangaren Shari’a.

ADVERTISEMENT

 

Ɓangaren Shari’a, yana ɗaya daga cikin ginshiƙan gwamnati Uku, da suka haɗa da ɓangarorin Zartarwa da Dokoki.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

 

Ɓangaren Shari’a a Nijeriya, yana da alhakin bayyana dokoki, kare kundin tsarin mulki, da kuma tabbatar da adalci. An tsara tsarin shari’a a karkashin jagorancin Kotun Ƙoli inda Alƙalin Alƙalan Nijeriya (CJN) ke kula da ita, sannan Kotun Ɗaukaka Ƙara da Manyan Kotuna a matakin jiha da tarayya.

 

Daga cikin manyan haƙƙoƙin da suka rataya akan ɓangaren Shari’a, akwai fassara kundin tsarin mulki da dokoki don amfani da su a shari’o’i. Sulhunta masu saɓani da kare haƙƙin ‘yan ƙasa da kuma tabbatar da cewa, sauran sassan gwamnati suna aiki a cikin iyakokin kundin tsarin mulki.

 

Amma, mu tambayi kanmu, wai me ke faruwa a ɓangaren Shari’a, ake samun hukuncin Shari’a ɗaya masu karo da juna?

 

An samu ruɗani a Kano a ranar Talata, 29 ga Mayu, 2024 bayan wani umarnin kotu guda biyu masu karo da juna game da taƙaddamar da ta taso kan sarautar Masarautar Kano tsakanin Sarki Muhammadu Sanusi na II da Aminu Ado Bayero, sarkin da aka sauke.

 

Yayin da Mai Shari’a S. Amobeda na Babbar Kotun Tarayya, Kano, ya umarci Sufeto Janar na ‘Yansanda, Kayode Egbetokun, da Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Kano, Hussain Gumel, da su tabbatar da cewa, an bai wa Aminu Ado Bayero dukkan haƙƙoƙin gata da ake bai wa sarakuna, nan take kuma, Mai Shari’a Amina Aliyu ta Babbar Kotun Jihar Kano ta hana ‘yansanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da Sojojin Nijeriya korar Muhammadu Sanusi na II, Sarkin Kano da aka dawo da shi kan kujerar sarautar.

 

Taƙaddamar dai ta fara ne a lokacin da gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sauke Bayero daga kan sarautar Masarautar Kano, tare da wasu Sarakuna huɗu na Rano, Bichi, Karaye da Gaya inda kuma ya mayar da Lamido Sanusi a matsayin Sarki bayan soke dokar da tsohon gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya yi amfani da ita wajen sauke shi daga kujerar mulki a shekarar 2020.

 

Da yake magana kan halin da ake ciki a Kano, wani lauya mazaunin Abuja, Kennedy Khanoba, yayin da yake tattaunawa da Jaridar PUNCH ya roƙi Shugaba Bola Tinubu da ya bar doka ta yi aiki, a ajiye maganar siyasa a gefe, yanzu doka tana hannun gwamnan jihar.

 

Har ila yau, Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya (NBA) ta nuna rashin jin daɗi game da hukunce-hukuncen da ke karo da juna daga kotuna.

 

Ƙungiyar lauyoyin ta yi wannan kira ne yayin da take yi wa ‘yan jarida bayani kafin Makon Shari’a na 2025, inda ta kuma yi kira da a yi gyare-gyare don daidaita shari’o’in kafin zaɓen dake tafe a ƙasar.

 

Sai dai, shugaban na NBA reshen Akure, ya yi karin haske da cewa, “wani lokacin, yanke hukuncin masu karo da juna, suna tasowa ne daga bambance-bambancen ra’ayoyin alkalai” kuma ya amince cewa Majalisar Shari’a ta Ƙasa (NJC) tana ƙoƙarin kawo ƙarshen wannan yanayi. Yayin da wasu masu ruwa da tsaki a ɓangaren Shari’a ke zargin ke zargin ɓangaren zartarwa da tsoma baki a Shari’o’in da suke da wani ra’ayi na musamman akai.

 

To, ko meye ke haifar da wannan hukunce-hukuncen masu bugu da juna?

Kotu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 - Ajuji

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.