• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Majalisar Dinkin Duniya Da ECOWAS Sun Yi Sabon Gargadi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben 2023: Majalisar Dinkin Duniya Da ECOWAS Sun Yi Sabon Gargadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Majalisar Dinkin Duniya (UN) da Kungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) sun gargadi Nijeriya game da rikicin zaben 2023.

Yayin da UN ta yi gargadin cewa, idan har abubuwa suka ci gaba da tabarbarewa a Nijeriya, to za a samu mummunan sakamako ga zaman lafiya da kwamciyar hankali a kasar baki daya, sannan kungiyar ECOWAS ta ce idan aka samu tashin hankali a Nijeriya, babu wata kasa a yankin Yammacin Afirka da za ta iya daukar ‘yan gudun hijirar Nijeriya.

  • Yadda Ake Kafa Kamfanin Burodi
  • An Watsa Shirin Bidiyo Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Bazara A Wurare Daban Daban Na Duniya

Sun dai yi wannan gargadin ne a garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato a wurin wani taro na bayar da horon sasantawa da hulda da hadakan kungiyoyin da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka fito daga yankin arewa ta tsakiya da arewa maso gabas kan dakile rikice-rikicen zaben 2023.
An bayar da rahoton cewa sama da mutum 30 ne suka rasa rayukansu, sannan da dama sun jikkata sakamakon rikice-rikicen zaben 2023 a wasu sassan Nijeriya.
Haka kuma an sa sha kai hare-hare a ofisoshin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), musamman a yankin kudu maso gabashin Nijeriya, wadanda yawancinsu suna da alaka da haramtacciyar kungiyar nan mai fafatukar kafa kasar Biafara (IPOB), lamarin da ya kai ga kashe ma’aikatan INEC da jami’an tsaro da dama.
Da take jawabi a wurin taron, wakiliyar ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da yammacin Afirka, Sa’adatu Sha’abu ta ce, “Idan har al’amura suka ci gaba da yin tsami a Nijeriya, za a samu mummunan sakamako ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkan yankin yammacin Afirka.”
Jami’in tsare-tsare na kungiyar ECOWAS, wanda ya kasance mai shiga tsakani Brown Odigie ya ja kunnen masu ruwa da tsaki kan gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da lumana.
Odigie ya kasance wakilin kwamishinan kungiyar ECOWAS kan harkokin siyasa, zaman lafiya da kuma tsaro, Abel Fatau ya bukaci dukkan ‘yan takara da jam’iyyunsu da su martaba yarjejeniyar zaman lafiya da suka sanya wa hannu da kuma ka’idojin zaben 2023.
Ya ce, “Wannan wani sasanci ne da ake yawan yi a kasashen da ke cikin kungiyar ECOWAS. Muna yin wannan lamari a Nijeriya ne, saboda Nijeriya ta kasance babbar mamba a kungiyar ECOWAS.
“Nijeriya na da dimbin al’umma. Zaben na iya haifar da rikici idan har ba a gudanar da shi yadda ya kamata ba. Kuma idan har aka samu rikici, zai iya shafar sauran kasashe makwabta saboda dinbin jama’an da Nijeriya take da su. Ina mai tabbatar muku da cewa babu wata kasa a cikin kungiyar ECOWAS da ke da karfin daukar ‘yan gudun hijira daga Nijeriya.”
Sakataren gamayyar kungiyoyin na kasa, Yusuf Dantalle ya bayyana cewa ‘yan saiyasa sukan shiga halin kaka-ni-ka-yi a lokacin da suka yi rashin nasara, saboda makudan kudaden da suke kashewa a zabe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASGargadiZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ake Kafa Kamfanin Burodi

Next Post

Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.