• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Majalisar Dinkin Duniya Da ECOWAS Sun Yi Sabon Gargadi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben 2023: Majalisar Dinkin Duniya Da ECOWAS Sun Yi Sabon Gargadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Majalisar Dinkin Duniya (UN) da Kungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) sun gargadi Nijeriya game da rikicin zaben 2023.

Yayin da UN ta yi gargadin cewa, idan har abubuwa suka ci gaba da tabarbarewa a Nijeriya, to za a samu mummunan sakamako ga zaman lafiya da kwamciyar hankali a kasar baki daya, sannan kungiyar ECOWAS ta ce idan aka samu tashin hankali a Nijeriya, babu wata kasa a yankin Yammacin Afirka da za ta iya daukar ‘yan gudun hijirar Nijeriya.

  • Yadda Ake Kafa Kamfanin Burodi
  • An Watsa Shirin Bidiyo Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Bazara A Wurare Daban Daban Na Duniya

Sun dai yi wannan gargadin ne a garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato a wurin wani taro na bayar da horon sasantawa da hulda da hadakan kungiyoyin da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka fito daga yankin arewa ta tsakiya da arewa maso gabas kan dakile rikice-rikicen zaben 2023.
An bayar da rahoton cewa sama da mutum 30 ne suka rasa rayukansu, sannan da dama sun jikkata sakamakon rikice-rikicen zaben 2023 a wasu sassan Nijeriya.
Haka kuma an sa sha kai hare-hare a ofisoshin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), musamman a yankin kudu maso gabashin Nijeriya, wadanda yawancinsu suna da alaka da haramtacciyar kungiyar nan mai fafatukar kafa kasar Biafara (IPOB), lamarin da ya kai ga kashe ma’aikatan INEC da jami’an tsaro da dama.
Da take jawabi a wurin taron, wakiliyar ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da yammacin Afirka, Sa’adatu Sha’abu ta ce, “Idan har al’amura suka ci gaba da yin tsami a Nijeriya, za a samu mummunan sakamako ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkan yankin yammacin Afirka.”
Jami’in tsare-tsare na kungiyar ECOWAS, wanda ya kasance mai shiga tsakani Brown Odigie ya ja kunnen masu ruwa da tsaki kan gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da lumana.
Odigie ya kasance wakilin kwamishinan kungiyar ECOWAS kan harkokin siyasa, zaman lafiya da kuma tsaro, Abel Fatau ya bukaci dukkan ‘yan takara da jam’iyyunsu da su martaba yarjejeniyar zaman lafiya da suka sanya wa hannu da kuma ka’idojin zaben 2023.
Ya ce, “Wannan wani sasanci ne da ake yawan yi a kasashen da ke cikin kungiyar ECOWAS. Muna yin wannan lamari a Nijeriya ne, saboda Nijeriya ta kasance babbar mamba a kungiyar ECOWAS.
“Nijeriya na da dimbin al’umma. Zaben na iya haifar da rikici idan har ba a gudanar da shi yadda ya kamata ba. Kuma idan har aka samu rikici, zai iya shafar sauran kasashe makwabta saboda dinbin jama’an da Nijeriya take da su. Ina mai tabbatar muku da cewa babu wata kasa a cikin kungiyar ECOWAS da ke da karfin daukar ‘yan gudun hijira daga Nijeriya.”
Sakataren gamayyar kungiyoyin na kasa, Yusuf Dantalle ya bayyana cewa ‘yan saiyasa sukan shiga halin kaka-ni-ka-yi a lokacin da suka yi rashin nasara, saboda makudan kudaden da suke kashewa a zabe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASGargadiZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ake Kafa Kamfanin Burodi

Next Post

Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

19 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

20 hours ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

21 hours ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
Next Post
Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.