• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, (PDPCC) ya bukaci hukumar yaki da karya tattalin arzikin kasa da ha’inci (EFCC) da hukumar yaki da safarar miyagun kwayoyi (NDLEA) su gaggauta cafke dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu kan zargin da ake masa na safarar miyagun kwayoyi da yin ruf da ciki da dukiyar jiha.

A wani taron manema labarai da suka yi a yau Lahadi a Abuja, PDP ta ce bayan an kama Tinubun, a hanzarta gurfanar da shi a gaban kuliya kan wadannan zarge-zargen.

Kakakin kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar, Mista Daniel Bwala ya bukaci NDLEA ta nemi cikakken bayani daga Tinubu don ya fayyace bayanai kan dalilan da suka janyo har hukumomi a kasar Amurka suka kwace masa Dala 460,000.

Bwala, kazalika ya yi tir da wata kungiyar da ya ce Tinubu ta kafa, da ya ce kamar kungiya ce ta mayakan sa-kai, sai ya nemi hukumomin tsaro da su cafke da gurfanar da duk wani da ya kasance cikin kungiyar mai suna ‘Jagaban Army’.

Sun Yi zargin cewa an kafa kungiyar ce kawai domin kawo yamutsi da firgici gabanin da yayin zabuka.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

Ya kara da cewa mambobin jam’iyyar adawa da dama suna fuskantar kalubale da barazana kashi-kashi gabanin zaben 2023.

Wani ma daga cikin masu magana da kwamitin yakin zaben na PDP, Phrank Shaibu, shi ma ya zargi Tinubu da cewa har yanzu yana cikin zargin harkallar kwayoyi.

Kazalika kwamitin ya zargi Tinubu Wanda tsohon gwamnan Jihar Legas ne da yin sama da fadi da dukiyar jihar a lokacin da yake matsayin gwamna.

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya ne bayanai suka karade cewa wata kotu a Amurka ta kwace wasu dalolin Amurka daga asusun Tinubu a yankin arewacin Illinois kan zargin alaka da fataucin kwayoyi.

Sai dai kuma takardun bayanan ba su ba da wasu bayanai ko tabbatar da cewa an yi wa Tinubu shari’a ba, ko kuma yana da alaka da wata kungiyar fataucin kwayoyi.

Takardun sun kuma nuna cewa an yi wannan shari’a ce shekaru 30 da suka gabata.

A cewar bayanan, wannan yanayi ne ya tursasa wa Tinubu sadaukar da kudaden da yawansu ya kai dala 460,000 a daya daga cikin asusun bankunansa 10.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Barcelona Ta Dawo Cikin Hayyacinta – Cewar Laporta

Next Post

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

Related

Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

2 weeks ago
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

1 month ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

1 month ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

2 months ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

2 months ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

2 months ago
Next Post
Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.