• Leadership Hausa
Monday, March 27, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
2 months ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, (PDPCC) ya bukaci hukumar yaki da karya tattalin arzikin kasa da ha’inci (EFCC) da hukumar yaki da safarar miyagun kwayoyi (NDLEA) su gaggauta cafke dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu kan zargin da ake masa na safarar miyagun kwayoyi da yin ruf da ciki da dukiyar jiha.

A wani taron manema labarai da suka yi a yau Lahadi a Abuja, PDP ta ce bayan an kama Tinubun, a hanzarta gurfanar da shi a gaban kuliya kan wadannan zarge-zargen.

Kakakin kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar, Mista Daniel Bwala ya bukaci NDLEA ta nemi cikakken bayani daga Tinubu don ya fayyace bayanai kan dalilan da suka janyo har hukumomi a kasar Amurka suka kwace masa Dala 460,000.

Bwala, kazalika ya yi tir da wata kungiyar da ya ce Tinubu ta kafa, da ya ce kamar kungiya ce ta mayakan sa-kai, sai ya nemi hukumomin tsaro da su cafke da gurfanar da duk wani da ya kasance cikin kungiyar mai suna ‘Jagaban Army’.

Sun Yi zargin cewa an kafa kungiyar ce kawai domin kawo yamutsi da firgici gabanin da yayin zabuka.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-ɗuminsa: Kwamishinan Harkokin Addini Na Jihar Sokoto Ya Rasu

Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

Ya kara da cewa mambobin jam’iyyar adawa da dama suna fuskantar kalubale da barazana kashi-kashi gabanin zaben 2023.

Wani ma daga cikin masu magana da kwamitin yakin zaben na PDP, Phrank Shaibu, shi ma ya zargi Tinubu da cewa har yanzu yana cikin zargin harkallar kwayoyi.

Kazalika kwamitin ya zargi Tinubu Wanda tsohon gwamnan Jihar Legas ne da yin sama da fadi da dukiyar jihar a lokacin da yake matsayin gwamna.

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya ne bayanai suka karade cewa wata kotu a Amurka ta kwace wasu dalolin Amurka daga asusun Tinubu a yankin arewacin Illinois kan zargin alaka da fataucin kwayoyi.

Sai dai kuma takardun bayanan ba su ba da wasu bayanai ko tabbatar da cewa an yi wa Tinubu shari’a ba, ko kuma yana da alaka da wata kungiyar fataucin kwayoyi.

Takardun sun kuma nuna cewa an yi wannan shari’a ce shekaru 30 da suka gabata.

A cewar bayanan, wannan yanayi ne ya tursasa wa Tinubu sadaukar da kudaden da yawansu ya kai dala 460,000 a daya daga cikin asusun bankunansa 10.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Barcelona Ta Dawo Cikin Hayyacinta – Cewar Laporta

Next Post

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

Related

Da Ɗumi-ɗuminsa: Kwamishinan Harkokin Addini Na Jihar Sokoto Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗuminsa: Kwamishinan Harkokin Addini Na Jihar Sokoto Ya Rasu

3 days ago
Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Adeleke A Matsayin Gwamnan Osun

3 days ago
Tsohon Kakakin Majalisar Gombe, Nasiru Nono Ya Rasu A Hatsarin Mota
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Kakakin Majalisar Gombe, Nasiru Nono Ya Rasu A Hatsarin Mota

4 days ago
Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Hana Fita A Fadin Jihar 
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Hana Fita A Fadin Jihar 

6 days ago
Da Dumi-Dumi: Gwamna Bala Ya Doke Tsohon Hafsan Sojin Sama Ya Lashe Zaben Bauchi
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Dumi-Dumi: Gwamna Bala Ya Doke Tsohon Hafsan Sojin Sama Ya Lashe Zaben Bauchi

1 week ago
Ganduje Ya Sanya Dokar Hana Fita Bayan Sanar Da Nasarar Lashe Zaben Abba Gida-Gida
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Sanya Dokar Hana Fita Bayan Sanar Da Nasarar Lashe Zaben Abba Gida-Gida

1 week ago
Next Post
Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron CDF Na Bana

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Taron CDF Na Bana

March 27, 2023
Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

Kafar CGTN Ta Gabatar Da Jerin Bidiyo Don Yin Bayani Game Da Tsarin Demokuradiyyar Kasar Sin

March 27, 2023
Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

Kafa Dangantakar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Honduras Ya Sake Tabbatar Da Manufar Sin Daya Tak A Duniya

March 27, 2023
Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

Gwamna Mai Barin Gado Da Zababbe Sun Fara Cacar Baki Kan Albashin Ma’aikata A Taraba

March 27, 2023
Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

Abdulaziz Yari Ya Bada Tallafin Tirela 240 Na Abincin Azimi A Zamfara

March 27, 2023
2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

2023: INEC Ta Sanar Da Ranar Mika Wa Zababbun Gwamnoni Takardar Shaidar Lashe Zabe

March 27, 2023
SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

SERAP Ta Nemi INEC Ta Hukunta Gwamnoni Kan Bangar Siyasa

March 27, 2023
DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Cafke Tsohon Soja Da Lauya Da Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 27, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 3 A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 5

March 27, 2023
PDP Ta Dakatar Da Tsofaffin Ministoci 2 Da Wasu 5 Kan Yi Wa Jam’iyyar Zagon-Kasa

PDP Ta Dakatar Da Shugabanta Na Kasa Kan Zargin Yi Wa Jam’iyyar Adawa Aiki

March 26, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.