ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
pdp

Kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, (PDPCC) ya bukaci hukumar yaki da karya tattalin arzikin kasa da ha’inci (EFCC) da hukumar yaki da safarar miyagun kwayoyi (NDLEA) su gaggauta cafke dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu kan zargin da ake masa na safarar miyagun kwayoyi da yin ruf da ciki da dukiyar jiha.

A wani taron manema labarai da suka yi a yau Lahadi a Abuja, PDP ta ce bayan an kama Tinubun, a hanzarta gurfanar da shi a gaban kuliya kan wadannan zarge-zargen.

Kakakin kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar, Mista Daniel Bwala ya bukaci NDLEA ta nemi cikakken bayani daga Tinubu don ya fayyace bayanai kan dalilan da suka janyo har hukumomi a kasar Amurka suka kwace masa Dala 460,000.

ADVERTISEMENT

Bwala, kazalika ya yi tir da wata kungiyar da ya ce Tinubu ta kafa, da ya ce kamar kungiya ce ta mayakan sa-kai, sai ya nemi hukumomin tsaro da su cafke da gurfanar da duk wani da ya kasance cikin kungiyar mai suna ‘Jagaban Army’.

Sun Yi zargin cewa an kafa kungiyar ce kawai domin kawo yamutsi da firgici gabanin da yayin zabuka.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

Ya kara da cewa mambobin jam’iyyar adawa da dama suna fuskantar kalubale da barazana kashi-kashi gabanin zaben 2023.

Wani ma daga cikin masu magana da kwamitin yakin zaben na PDP, Phrank Shaibu, shi ma ya zargi Tinubu da cewa har yanzu yana cikin zargin harkallar kwayoyi.

Kazalika kwamitin ya zargi Tinubu Wanda tsohon gwamnan Jihar Legas ne da yin sama da fadi da dukiyar jihar a lokacin da yake matsayin gwamna.

Idan za a iya tunawa a kwanakin baya ne bayanai suka karade cewa wata kotu a Amurka ta kwace wasu dalolin Amurka daga asusun Tinubu a yankin arewacin Illinois kan zargin alaka da fataucin kwayoyi.

Sai dai kuma takardun bayanan ba su ba da wasu bayanai ko tabbatar da cewa an yi wa Tinubu shari’a ba, ko kuma yana da alaka da wata kungiyar fataucin kwayoyi.

Takardun sun kuma nuna cewa an yi wannan shari’a ce shekaru 30 da suka gabata.

A cewar bayanan, wannan yanayi ne ya tursasa wa Tinubu sadaukar da kudaden da yawansu ya kai dala 460,000 a daya daga cikin asusun bankunansa 10.

pdp
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Ganduje Ya Ambaci Sunan Sarki Sanusi Da Matsayin Sarkin Kano

May 5, 2026
Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru
Siyasa

Gwamnatin Jigawa Ta Bayar Da Umarnin Bincikar Tsohon Gwamnan Jihar Badaru

April 25, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.