• English
  • Business News
Friday, June 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙaddamar Da Ba Da Sabon Fasfo A Katsina, Ta Buɗe Babban Ofishinta

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Ƙaddamar Da Ba Da Sabon Fasfo A Katsina, Ta Buɗe Babban Ofishinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Talata, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), ta buɗe katafaren babban ofishinta na Jihar Katsina tare da ƙaddamar da bayar da sabon ingantaccen fasfo na zamani a yankin.

Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola ne ya buɗe ofishin tare da shugaban hukumar ta NIS, CGI Idris Isah Jere a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da aka gudanar.

  • TARON LEADERSHIP: Buhari Ya Sauya Fasalin Tsarin Tattalin Arzikin Nijeriya —Ministan Abuja
  • Shugaban NIS Ya Sake Gargadin Marasa Gaskiya A Kan Harkokin Fasfo

Da yake jawabi a wurin, shugaban NIS, Isah Jere ya bayyana cewa, samar da sabon ingantaccen fasfo na zamani yana da matuƙar muhimmanci a cikin ayyukan da hukumar take yi wa ‘yan ƙasa, yana mai cewa, “tabbas muna sane da irin ƙalubalen da ‘yan ƙasa ke fuskanta wajen neman fasfo a lokutan baya, amma muna tabbatar muku da cewa bisa ƙoƙarin da muke yi daban-daban, kamar ƙaddamar da bayar da fasfo na zamani a Jihar Katsina, ba da jimawa ba waɗannan ƙalubalen za su kau. Muna ci gaba da ƙoƙarin buɗe ofisoshin karɓa da shigar da bayanan masu neman fasfo a jihar domin rage cunkoso. A kwanan nan za a kammala aikin ofishin na Daura tare da ƙaddamar da shi. Tuni aka samar da kayan aikin yin sabon fasfon a Katsina, nan da ‘yan kwanaki kaɗan komai zai yi daidai a fara gudanar da aiki, muna sa rai har da na Daura ma.”

NIS
NIS: Ziyarar da tawagar ta kai wa Gwamna Bello Masari a gidan gwamnatin Katsina

Isah Jere ya bayyana cewa bisa ƙaddamar da bayar da sabon fasfon na zamani, haƙiƙa za a magance tafiyar hawainiyar da ake samu wajen neman fasfo, matuƙar dai mai nema ya bi ƙa’idojin da aka shimfiɗa, ciki har da tabbatar da cewa ya gabatar da buƙatarsa ta shafin intanet tare da biyan kuɗi ta nan da kuma tabbatar da cewa bayanansa na fasfo sun yi daidai da na lambar shaidarsa ta ɗan ƙasa (NIN).

“Fasfo yana da matakai daban-daban, akwai mai aiki na tsawon shekara 10, wannan na waɗanda suka zama baligai ne da aka samar musu don magance yawan kai-komonsu a ofisoshin fasfo. Haka nan akwai sauran matakai wanda mai neman fasfo zai iya zaɓa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

“Sabon fasfon na zamani an yi shi ne da fasahar takardun zamani masu inganci wanda ruwa ba ya lalatawa, sannan yana da ƙarin alamomin tsaro guda 25 fiye da wanda ake bayarwa kafin ɓullo da shi (electronic passport). Shi wannan sabon da ake bayarwa shi ne ake yayi a halin yanzu a ɓangaren fasahar samar da fasfo a duniya, yana da ƙarko da kuma sauƙin amfani. Sannan zai yi matuƙar wahala a iya yin jabunsa saboda duk wanda ya yi yunƙurin haka ba wai kawai ba zai yiwu masa ba ne, a’a, da ya fara za a gano shi. Nijeriya ce ƙasa ta farko a duk faɗin Afirka da ta fara yin ƙaura zuwa sabon yayin na fasfo.” In ji Jere.

NIS
NIS: Minista Ogbeni Aregbesola, CGI Idris Isah Jere da wani babban jami’in tsaron fararen hula a bikin

Shugaban na NIS, ya kuma ƙara da cewa, ana ci gaba da buɗe ofisoshin bayar da sabon fasfon, har ila yau ana ci gaba da bayar da tsohon shi ma har zuwa lokacin da za a mayar da kowace cibiyar fasfo ta zama mai bayar da sabon na zamani.

Haka nan ya yi nuni da cewa, buɗe sabon katafaren ofishin NIS na Jihar Katsina, ya sake tabbatar da irin duƙufar da hukumar ta yi wajen kula da jindaɗin jami’anta. A cewarsa, “wannan zai ƙara bunƙasa ƙwazonsu su ci gaba da yin aiki tuƙuru. Ina kuma kira tare da tunatar da cewa, bisa la’akari da yanayin tattalin arzikin ƙasa, ya zama wajibi mu kula sosai da abin da muke da shi tare da yin kyakkyawan amfani da wannan sabon ginin. Wajibi ne a kula da matakan riga-kafi a kowane lokaci.”

Ya gode wa Ministan cikin gida, Ogebeni Aregbesola bisa goyon bayan da yake bai wa NIS tun daga lokacin da aka naɗa shi minista. Haka nan ya yi godiya ga shugaban ƙasa bisa rattaba hannun amincewa a takardun hukumar waɗanda suka zamo silar samun nasarorin da ake gani.

Har ila yau, shugaban na NIS, CGIS Idris Isah Jere, ya yaba da irin haɗin kan da suke samu daga sauran abokan aiki na hukumomi daban-daban da ita kanta Gwamnatin Jihar Katsina, da sarakuna da sojoji da sauransu.

  • https://leadership.ng/nis-redeploys-69-senior-officers/nigeria-immigration-service/

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Mahara Sun Kashe DPO Da Wasu A Benue

Next Post

Cikin Shekaru 3 Da Suka Gabata Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Yaki Da Annobar COVID-19 

Related

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 
Manyan Labarai

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

1 hour ago
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

2 hours ago
Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo

3 hours ago
Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
Manyan Labarai

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

4 hours ago
An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya
Manyan Labarai

An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

5 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

5 hours ago
Next Post
Cikin Shekaru 3 Da Suka Gabata Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Yaki Da Annobar COVID-19 

Cikin Shekaru 3 Da Suka Gabata Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Yaki Da Annobar COVID-19 

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 16/05/2025

GORON JUMA’A 20-06-2025

June 20, 2025
Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

June 20, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

June 20, 2025
Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo

June 20, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

June 20, 2025
Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6

Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6

June 20, 2025
Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

June 20, 2025
An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

June 20, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

June 20, 2025
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

June 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.