ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Lalata Kayayyakin Gwamnati A Binuwe

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
11 months ago
Ta’addanci

An rawaito cewa sojoji sun kama mutum biyu da ake zargi da lalata kayayyaki a garin Otukpo, karamar hukumar Otukpo, jihar Binuwe.

 

An ce an kama wadanda ake zargin ne yayin da suke lalata kayan aiki da abubuwan more rayuwa a wajen masana’antar Binuwe Burnt Bricks da ke Otukpo.

ADVERTISEMENT
  • Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Majiya ta ce wadanda ake zargin sun kai hari kamfanin da ke kan babbar hanyar tarayya a Otukpo a daren Asabar, amma sojoji da ke wurin sun kamo su.

 

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

An bayyana sunayen wadanda ake zargin Wilson Egbanga mai shekara (16) da Okoh Akoja mai shekara (40), wadanda dukkaninsu suka ce mazauna Karamar Hukumar Otukpo ne.

 

Wani mazaunin Otukpo, da aka ambaci sunansa Adaji, ya shaida wa wakilinmu cewa wasu mutane da ke wurin da suka ga wadanda ake zargin sun kai rahoto ga sojoji, wadanda suka dauki mataki nan take, wanda ya kai ga kama su.

 

Shugaban Karamar Hukumar Otukpo, Madwell Ogiri, ya tabbatar da kama wadanda ake zargin lalata kayayyaki, inda ya ce an mika su ga jami’an Hukumar Tsaro ta Jiha (DSS) a Otukpo.

 

Shugaban, wanda ya yi magana ta hanyar mai ba shi labarai, Joshua Otene, ya ce: “An kama wadanda ake zargin a wurin aikinsu,” sannan ya jera kayan da aka samu a hannunsu, ciki har da karafa da yawa, bututun gas biyu masu girma, da karamin bututun gas din da aka hada da hoses da ake zargin an yi amfani da su wajen yanka karfe.

 

Ya kara da cewa, “A yayin tambayoyin farko, wadanda ake zargin sun ce an ja hankalinsu zuwa aikata laifin ne ta hannun wani mutum mai suna Omagbo, wanda ake cewa yana tukin motar Hi-Jet fara a cikin al’ummomin da ke iyaka da wajen Binuwe Burnt Bricks.

 

“Amma shugaban kungiyar da ake zargin, har yanzu yana bacewa.”

 

Lokacin da aka tuntubi mataimakin kwamandan DSS na Otukpo, Mr Aba Bashi, ta wayar tarho, ya tabbatar da kama wadanda ake zargin sannan ya ce har yanzu suna hannunsu kuma za a mika su zuwa Makurdi nan ba da jimawa ba.

 

“Gaskiya ne cewa sojoji sun kawo mutane biyu da ake zargin lalata kayayyaki zuwa ofishinmu. Za a mika su zuwa Makurdi nan ba da jimawa ba,” in ji Bashi.

 

Lalacewar kayayyakin more rayuwa na daga cikin manyan barazanar da ke kalubalantar ci gaban Nijeriya da harkokin masana’antu, inda yake lalata dukiyar jama’a kuma yana kawo cikas ga kokarin bunkasa kasa.

Binuwe Burnt Bricks an kafa shi ne a zamanin marigayi Gwamna Aper Aku, amma ya kasance a kashe shekaru da dama, inda wasu kayan aiki da abubuwan more rayuwa suka lalace.

 

Kokarin samun martanin Kwamandan ‘Yansanda na Jihar bai samu nasara ba, domin kakakin rundunar, DSP Udeme Edet, bai amsa kiran waya ko sakonnin waya da aka tura mata zuwa wayarta ba har lokacin kammala wannan rahoto.

Sojoji
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Sojoji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.