• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Kwamitin Lura Da Takara Da Sin Da Amurka Ta Kafa Ba Zai Haifar Da Dan Mai Ido Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sabon Kwamitin Lura Da Takara Da Sin Da Amurka Ta Kafa Ba Zai Haifar Da Dan Mai Ido Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ’yan kwanakin nan, majalissar wakilan Amurka ta kafa wani kwamiti da ta ce zai lura da batutuwa masu nasaba da takarar da kasar ke yi da kasar Sin, har ma majalissar na ganin kwamitin zai iya zama wata garkuwa, da abun da ya kira hanyoyi mabanbanta da Sin ke zama barazana ga Amurka.

Duk da cewa aikin da aka dorawa kwamitin bai wuce na bincike da kuma ba da shawara ba, kafa shi wata manuniya ce ga kudurin siyasar Amurka, na nacewa tunanin cacar baka tsakanin ta da Sin.

  • Sin Ta Tallafawa Makarantun Sudan Ta Kudu Da Litattafai Sama Da 300,000

Masharhanta da dama na ganin an kafa kwamitin ne domin karfafa matakan gwamnatin Amurka mai ci na dakile kasar Sin, karkashin amincewar majalissar dokokin kasar, da goyon bayan gwamnatin shugaba Joe Biden, wanda ko shakka babu cikin tsawon lokaci, tasirin hakan zai ci gaba da illata alakar Sin da Amurka.

Idan mun waiwayi tarihi, za mu ga bayan aukuwar harin 11 ga watan Satumban 2001, Amurka ta mayar da batun yaki da ta’addanci sahun gaba, a manufofinta na tsaro da diflomasiyyar kasashen waje. Daga bisani kuma a shekarar 2017, gwamnatin tsohon shugaban kasar Donald Trump ta bullo da abun da ta kira matakan tsaron kasa, wanda karkashin hakan ta ayyana kasar Sin a matsayin “Muhimmiyar abokiyar takara” ga Amurka. Tun daga wannan lokacin ne kuma, Amurka ke ci gaba da bunkasa wannan manufa ta fuskoki daban daban.

To sai dai abun tambaya a nan shi ne, tun daga waccan manufa ta tsaron kasa, wadda karkashinta Amurka ta rika yakar kasashe daban daban, tare da haifar da mummunan tasirin yaki kan miliyoyin fararen hula, har zuwa dokar ayyana Sin a matsayin barazana ga Amurka, wacce manufa ce a cikin su ta haifarwa Amurka wani alfanu?

Labarai Masu Nasaba

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Sanin kowa ne cewa, manufar Amurka ta yake-yake, da daura damarar yin takara maras adalci, ko rarraba kan yankunan duniya zuwa rukunoni, da maida wasu sassa saniyar ware, ba abun da suka haifarwa kasar sai koma baya, da kara jefa al’ummun duniya cikin mummunan yanayi.

Don haka dai ya kamata Amurka ta yi karatun ta nutsu, ta yi watsi da manufofin wariya da nuna kyama, ko yunkurin dakile kasar Sin ta dukkanin fannoni, kafin hakan ya kai ga haifar da mummunan sakamako da zai jefa Amurka cikin halin matsin tattalin arziki, tare da gurgunta alaka da moriyar sassan biyu. (Saminu Hassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Tallafawa Makarantun Sudan Ta Kudu Da Litattafai Sama Da 300,000

Next Post

CBN Da ‘Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin  Kudi   

Related

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

1 hour ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

2 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

4 hours ago
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157
Daga Birnin Sin

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

5 hours ago
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

1 day ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

1 day ago
Next Post
CBN Da ‘Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin  Kudi    

CBN Da 'Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin  Kudi   

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.