• Leadership Hausa
Saturday, March 25, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Kwamitin Lura Da Takara Da Sin Da Amurka Ta Kafa Ba Zai Haifar Da Dan Mai Ido Ba

by CMG Hausa
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sabon Kwamitin Lura Da Takara Da Sin Da Amurka Ta Kafa Ba Zai Haifar Da Dan Mai Ido Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ’yan kwanakin nan, majalissar wakilan Amurka ta kafa wani kwamiti da ta ce zai lura da batutuwa masu nasaba da takarar da kasar ke yi da kasar Sin, har ma majalissar na ganin kwamitin zai iya zama wata garkuwa, da abun da ya kira hanyoyi mabanbanta da Sin ke zama barazana ga Amurka.

Duk da cewa aikin da aka dorawa kwamitin bai wuce na bincike da kuma ba da shawara ba, kafa shi wata manuniya ce ga kudurin siyasar Amurka, na nacewa tunanin cacar baka tsakanin ta da Sin.

  • Sin Ta Tallafawa Makarantun Sudan Ta Kudu Da Litattafai Sama Da 300,000

Masharhanta da dama na ganin an kafa kwamitin ne domin karfafa matakan gwamnatin Amurka mai ci na dakile kasar Sin, karkashin amincewar majalissar dokokin kasar, da goyon bayan gwamnatin shugaba Joe Biden, wanda ko shakka babu cikin tsawon lokaci, tasirin hakan zai ci gaba da illata alakar Sin da Amurka.

Idan mun waiwayi tarihi, za mu ga bayan aukuwar harin 11 ga watan Satumban 2001, Amurka ta mayar da batun yaki da ta’addanci sahun gaba, a manufofinta na tsaro da diflomasiyyar kasashen waje. Daga bisani kuma a shekarar 2017, gwamnatin tsohon shugaban kasar Donald Trump ta bullo da abun da ta kira matakan tsaron kasa, wanda karkashin hakan ta ayyana kasar Sin a matsayin “Muhimmiyar abokiyar takara” ga Amurka. Tun daga wannan lokacin ne kuma, Amurka ke ci gaba da bunkasa wannan manufa ta fuskoki daban daban.

To sai dai abun tambaya a nan shi ne, tun daga waccan manufa ta tsaron kasa, wadda karkashinta Amurka ta rika yakar kasashe daban daban, tare da haifar da mummunan tasirin yaki kan miliyoyin fararen hula, har zuwa dokar ayyana Sin a matsayin barazana ga Amurka, wacce manufa ce a cikin su ta haifarwa Amurka wani alfanu?

Labarai Masu Nasaba

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

Sanin kowa ne cewa, manufar Amurka ta yake-yake, da daura damarar yin takara maras adalci, ko rarraba kan yankunan duniya zuwa rukunoni, da maida wasu sassa saniyar ware, ba abun da suka haifarwa kasar sai koma baya, da kara jefa al’ummun duniya cikin mummunan yanayi.

Don haka dai ya kamata Amurka ta yi karatun ta nutsu, ta yi watsi da manufofin wariya da nuna kyama, ko yunkurin dakile kasar Sin ta dukkanin fannoni, kafin hakan ya kai ga haifar da mummunan sakamako da zai jefa Amurka cikin halin matsin tattalin arziki, tare da gurgunta alaka da moriyar sassan biyu. (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Tallafawa Makarantun Sudan Ta Kudu Da Litattafai Sama Da 300,000

Next Post

CBN Da ‘Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin  Kudi   

Related

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

1 hour ago
Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

2 hours ago
An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva
Daga Birnin Sin

An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

2 hours ago
Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Daina Muzgunawa Kamfanonin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Daina Muzgunawa Kamfanonin Waje

20 hours ago
Kamata Ya Yi Amurka Ta Nemi Amincewa Daga Kasa Da Kasa Kafin Komawar Ta Hukumar UNESCO
Daga Birnin Sin

Kamata Ya Yi Amurka Ta Nemi Amincewa Daga Kasa Da Kasa Kafin Komawar Ta Hukumar UNESCO

21 hours ago
CMG Ta Hada Kai Da Manyan Kafafen Yada Labaran Kasashen Afirka Biyar Don Kaddamar Da Wani Shirin TV Mai Suna “More Ci Gaba Tare”
Daga Birnin Sin

CMG Ta Hada Kai Da Manyan Kafafen Yada Labaran Kasashen Afirka Biyar Don Kaddamar Da Wani Shirin TV Mai Suna “More Ci Gaba Tare”

23 hours ago
Next Post
CBN Da ‘Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin  Kudi    

CBN Da 'Yansanda Za Su Sa Kafar Wando Daya Da Masu Sayar Da Sabbin  Kudi   

LABARAI MASU NASABA

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

Mun Kammala Nazari Kan Sakamakon Zaben Gwamnoni – INEC

March 25, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 4

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 4

March 25, 2023
An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

An Bude Dandalin Tattauna Harkokin Samar Da Ci Gaba Na Kasar Sin

March 25, 2023
Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

Burina Masu Basira Su Rika Amfana Da Basirarsu -Haidar Blog

March 25, 2023
Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

Rukunin Na’urori Na Biyar Na Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta “Lower Kefu Gorge” Dake Zambiya Sun Fara Aiki

March 25, 2023
An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

An Yi Zaman Taron “Kare Hakkin ‘Yan Kananan Kabilu A Sabon Zamani” A Geneva

March 25, 2023
Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

Ra’ayoyin Jam’iyyu Kan Nassarar Abba A Kano

March 25, 2023
Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

Tarihin Zaben Kano: Hannun Karba, Hannun Mayarwa

March 25, 2023
Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

Falalar Ramadan Da Wasu Hukunce-hukuncen Azumi

March 25, 2023
Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

Muna Samun Tallafi Daga Sarkin Noman Masarautar Gaya – Kungiyar Manoman

March 25, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.