• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Bayar Da Sabbin Kudi Ko Mu Kwace Takardun Shaidar Mallakarku – Zulum Ga Bankuna A Borno

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Ku Bayar Da Sabbin Kudi Ko Mu Kwace Takardun Shaidar Mallakarku – Zulum Ga Bankuna A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya gargadi bankuna a jihar cewa su bayar da sabbin kudade a na’urorin cire kudi na ATM don rage karancin kudaden ga jama’a, idan ba haka ba kuma gwamnatin jihar za ta kwace takardun mallakar filayen bankunan har sai idan bincike ya tabbatar cewa matsalar daga bankin CBN take.

Zulum ya yi wannan gargadin ne a ranar Juma’a a Maiduguri lokacin da yake rangadin rassan bankunan, domin ganewa idonsa yadda karancin takardun sabbin kudin ya jefa jama’a cikin mawuyacin hali a jihar, ta hanyar dogayen layuka a ATM ya tsananta a cikin rashin tabbas.

  • Zulum Ya Karbi ‘Yan Gudun Hijira 1,300 Daga Kamaru
  • Zulum Ya Kai Wa Majinyata Ziyarar Ba-Zata Cikin Dare A Wasu Asibitocin Jihar

“Duk wani banki a jihar Borno wanda yaki loda sabbin kudi a ATM dinsa, kuma bai damu da halin da jama’a suke ciki ba, tare da kin zuba isasshen kudi domin saukaka wa al’ummarmu radadin da suke ciki ba, to za mu soke takardar mallakarsu nan take. Face bankunan da bincike ya nuna suna da wata matsala ta daban.” in ji Zulum.

Kafin wannan matakin, Gwamna Zulum ya nuna rashin jindadin sa dangane da yadda daruruwan jama’a ke yin dafifi a layukan ATM a bankuna domin cire sabbin kudaden.

“Kamar yadda kuke gani a nan, maras gata ne kawai zaka iya gani a kan layi; ban ga masu kudi anan ba. Kuma an ce mutane da yawa suna nan tun karfe 3:00 na asuba, wasu ko abinci ba su ci ba. Sannan kuma da sabbi da tsoffin takardun Naira ba a samu, kuma hakan na yin illa ga harkokin kasuwanci a jihar Borno, saboda jama’a su na shan wahala.” Zulum ya nanata.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Gwamnan ya ci gaba da cewa: “Yanzu mun saki albashin kusan Naira biliyan 5 amma bankuna ba su da kudi, wasu na’urorin ATM din ba sa aiki. Kuma ba mu da matsala da manufar CBN ko ka’idar cire kudi, sun ce kowane mutum zai iya cire 20,000 a wuni, to amma me ya sa ba kowa ne zai iya samun wannan N20,000 ba?”

“A jiya ina garin Gubio mai yawan jama’a sama da 70,000 amma ba a iya samun Naira 100,000 a daukacin karamar hukumar, da sabbi da tsoffin kudin duka. Misali ragon 100,000 yanzu bai wuce 35,000 ba, saboda yadda ake neman kudi, al’amarin da ya jawo miyagun masu hannu da shuni na zuwa kauyuka don cutar talakawa.” Inji Zulum.

Gwamnan ya bukaci babban bankin Nijeriya (CBN) ya samar da sabbin takardun kudi a bankunan kasuwanci domin mutane su samu kudadensu.

“A yanzu haka a jihar Borno, na ziyarci na’urorin ATM a bankuna sama da goma amma babu kudi, mutane tsaye a layuka suna jiran tsammani.” in ji Zulum.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ATMBankunaBornoKarancin KudiZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Korafi Kan Cin Mutuncin Da Ake Yi Wa Binicius Junior

Next Post

Kyawawan Dabi’u, Tausayi, Jinkai Da Rahamar Manzon Allah (SAW)

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

47 minutes ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

1 hour ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

4 hours ago
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

7 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

8 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

10 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Kyawawan Dabi’u, Tausayi, Jinkai Da Rahamar Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.