ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ku Bayar Da Sabbin Kudi Ko Mu Kwace Takardun Shaidar Mallakarku – Zulum Ga Bankuna A Borno

by Muhammad Maitela
3 years ago
Zulum

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya gargadi bankuna a jihar cewa su bayar da sabbin kudade a na’urorin cire kudi na ATM don rage karancin kudaden ga jama’a, idan ba haka ba kuma gwamnatin jihar za ta kwace takardun mallakar filayen bankunan har sai idan bincike ya tabbatar cewa matsalar daga bankin CBN take.

Zulum ya yi wannan gargadin ne a ranar Juma’a a Maiduguri lokacin da yake rangadin rassan bankunan, domin ganewa idonsa yadda karancin takardun sabbin kudin ya jefa jama’a cikin mawuyacin hali a jihar, ta hanyar dogayen layuka a ATM ya tsananta a cikin rashin tabbas.

  • Zulum Ya Karbi ‘Yan Gudun Hijira 1,300 Daga Kamaru
  • Zulum Ya Kai Wa Majinyata Ziyarar Ba-Zata Cikin Dare A Wasu Asibitocin Jihar

“Duk wani banki a jihar Borno wanda yaki loda sabbin kudi a ATM dinsa, kuma bai damu da halin da jama’a suke ciki ba, tare da kin zuba isasshen kudi domin saukaka wa al’ummarmu radadin da suke ciki ba, to za mu soke takardar mallakarsu nan take. Face bankunan da bincike ya nuna suna da wata matsala ta daban.” in ji Zulum.

ADVERTISEMENT

Kafin wannan matakin, Gwamna Zulum ya nuna rashin jindadin sa dangane da yadda daruruwan jama’a ke yin dafifi a layukan ATM a bankuna domin cire sabbin kudaden.

“Kamar yadda kuke gani a nan, maras gata ne kawai zaka iya gani a kan layi; ban ga masu kudi anan ba. Kuma an ce mutane da yawa suna nan tun karfe 3:00 na asuba, wasu ko abinci ba su ci ba. Sannan kuma da sabbi da tsoffin takardun Naira ba a samu, kuma hakan na yin illa ga harkokin kasuwanci a jihar Borno, saboda jama’a su na shan wahala.” Zulum ya nanata.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Gwamnan ya ci gaba da cewa: “Yanzu mun saki albashin kusan Naira biliyan 5 amma bankuna ba su da kudi, wasu na’urorin ATM din ba sa aiki. Kuma ba mu da matsala da manufar CBN ko ka’idar cire kudi, sun ce kowane mutum zai iya cire 20,000 a wuni, to amma me ya sa ba kowa ne zai iya samun wannan N20,000 ba?”

“A jiya ina garin Gubio mai yawan jama’a sama da 70,000 amma ba a iya samun Naira 100,000 a daukacin karamar hukumar, da sabbi da tsoffin kudin duka. Misali ragon 100,000 yanzu bai wuce 35,000 ba, saboda yadda ake neman kudi, al’amarin da ya jawo miyagun masu hannu da shuni na zuwa kauyuka don cutar talakawa.” Inji Zulum.

Gwamnan ya bukaci babban bankin Nijeriya (CBN) ya samar da sabbin takardun kudi a bankunan kasuwanci domin mutane su samu kudadensu.

“A yanzu haka a jihar Borno, na ziyarci na’urorin ATM a bankuna sama da goma amma babu kudi, mutane tsaye a layuka suna jiran tsammani.” in ji Zulum.

Zulum
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Manzon Allah

Kyawawan Dabi’u, Tausayi, Jinkai Da Rahamar Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.