• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudummawar Mata A Harkar Samar Da Tsaro A Nijeriya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Gudummawar Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da muke yaba wa rundunonin tsaro ta bangaren gwamnati da na masu zaman kansu da suke aiki babbu kakkautawa don samar mana da cikakken tsaro tare da tabbatar da al’umma basu fuskantar wata matsala a sassan Nijeriya, muna yaba wa kungiyar maharba mata ta Jihar Taraba, wadda a ‘yan kwanakin nan ta nuna cewa, yaki da rashin tsaro ba abu ba ne da za a kebewa maza kawai suma mata na iya bayar da nasu gudunmawar.

Wadannan jaruman matan sun shiga kafada da kafada wajen yaki da ‘yan ta’addan da suka addabi al’umma jihar a ‘yan shekarun nan.

A Nijeriya tarihi ya nuna cewa, mata sun bayar da gaggarumar gudummawa wajen tabbatar da cikakken tsaro a cikin al’umma kuma bai kamata a manta gaba daya da hakan ba. Haka kuma mata na ci gaba da kasancewa a kan gaba a rundunonin tsaron Nijeriya, kamar Rundunar Sojin Nijeriya, ‘Yan sanda ‘Civil Defense’ da sauran rundunonin tsaro masu zaman kansu wajen yaki da matsalar tsaro a sassan kasar nan.

A kasar da mata suka kai fiye da mutum miliyan 200 wannan ba zai taba zama abin mamaki ga kowa ba. Tabbas rashin sanya mata a cikin tsarin jami’an tsaron kasa ba zai haifar da da mai ido ba musamman ganin yadda matsalar tsaro take kara karuwa.

A ‘yan kwanakin nan wasu jaruman mata suka hada hannu da takwarorin su maza a Jihar Taraba, don su yaki ayyukan ta’addanci da ta addabi yankunan, a halin yanzu zawarawan da ‘yan mata suna gangamin shiga wannan kungiyar, wannan wani lamari ne da ya kamata a yaba a kuma karfafa. Hare-haren da ake kai wa mata da yara kanana ya tilastawa matan shiga wannan kungiyar tare da daukar makamai don kare al’ummar su.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

Idan za a iya tunawa a watan Janairu na shekarar 2022 ne aka tura akalla sojoji mata fiye da 300 don aiki tare da sauran jami’an tsaron wajen yaki da ayyukan ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane da sauran ayyukan ta’addanci a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja a daidai lokacin lokacin da lamarin ayyukan ta’addancin ya ta’azzara.

Hakanan ma a shekarar 2018, shugaban rundunar sojojin Nijeriya na wancan lokacin Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai, ya karfafa mata yayin da ya kafa wata runduna ta musamman a yankin Afirika ta yamma.
Shigar da mata cikin tsarin harkar samar da tsaro a dukkan matakai a Nijeriya abu ne da ya karbu a sassan duniya kuma bai kamata a ce Nijeriya bata shiga sahu ba.

A lokacin da Buratai ya kafa Rundunar Sojoji Mata na Sojojin Nijeriya, ya bayyana cewa, “Za a ba rundunar dukkan goyon bayan da take bukata na shigar da mata a tsaron don su bayar da gudummawarsu na tabbatar da cikakkiyar tsaro a kasar mu.

Tarihi ya nuna irin nasarorin da mata suka samu a kokrin samar da tsaro a sassa daban-daban a Nijeriya. A wannan fannin tabass za mu iya tuna kungiyar tsaro da ake kira ‘Female amazons’ ta Jihar Filato, wadanda suke saukowa daga kan tsaunuka don kare al’ummar su daga hare-hare, haka kuma muna iya tunawa da Sarauniya Amina wadda ta jagoranci dakarun mahaifinta a yake-yake da aka yi wajen kare daular Zazzau.

Akwai kuma wasu mayaka mata a wasu kasashen yankin Afirka ta Yamma da suka hada da kasar Dahomey, a wanncan lokacin ana kiran matan da sunan “Black Sparta.” Sun yi kokarin fafatawa ba tare da tsoro ba wajen tunkarar yakin da ake yi da safarar mutane da sunan bayi.

Jarumai mata a sassan duniya sun nuna cewa, mata na iya bayar da gudummawar su wajen yaki da matsalar tsaro tare da tabbatar da tsaro a cikin al’umma.
An kuma samu rahotannin zaratan sojoji mata da suka fafata a cikin dakarun kasar ‘Kurdish Peshmerga’ a watan Yuni na shekarar 2014, inda suka shiga sahun dakarun da suka yaki don kwato garin Mosul na kasar Irak daga hannun kungiyar nan ta ‘yan ta’adda ta ISIS. Haka kuma bayan shekara 2 sun kuma kara fafatawa a karkashin dakaru mata fiye da 1,000 inda suka ceto garin Kirkuk da wasu rijiyoyin mai na kasar Irak daga hannun ‘yan ta’addar kungiyar ISIS.

A al’adance ana ganin mata a mastayin masu rauni da ba za su iya tafiya kafada da kafada da takwarorinsu maza ba amma a halihn yanzu al’amurra sun canza, yanzu mata na hada hannu da maza wajen dukkan ayyukan samar da tsaro a cikin al’umma.

A jawabin Gwamnan Jihar Kaduna a yayin da yake karbar matan da aka turo don yin aikin samar da tsrao a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja, ya ce, “tabbas duk abin da namiji zai iya yi mace ma za ta iya yin fiye da haka. Mun yi imanin matan Jihar Kaduna suna iya gabatar da ayyuka kamar maza suna kuma da kwarewar da ake bukata, za mu baku dukkan gudummawar da ake bukata don ku samu nasarar da ake bukata a wanan lokacin, muna alfahari da kasancewa ku, zuwan ku zai karfafa sauran matan jihar shiga aikin soja,” In ji shi.

Ba zamu manta da ‘Flying Officer Tolulope Arotile, da gudummawarta ga yaki da ta’addanci a yankin arewacin Nijeriya ba. Ita ce mace ta farko da ta fara tuka jirgin saman yaki na rundunar sojojin sama a Nijeriya. Nijeriya ta yi alhinin rasuwarta a shekarar 2021.

Haka kuma muna tuna mata da dama da suka rasa rayukansu ko suka bace a yayin da suke bautawa kasar haihuwarsu. Za a ci gaba da tunawa da su har abada.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamata Ya Yi A Daure Duk Dan Kasuwar Da Ke Shigo Da Tufafi Nijeriya Daga Kasar Waje —Dangote

Next Post

Yadda Wani Tsohon A Kauyen Liujiayuan Ya Bude Sabon Babin Shiga Wasanni Na Zamani

Related

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

31 minutes ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

3 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

3 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

15 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

16 hours ago
Next Post
Yadda Wani Tsohon A Kauyen Liujiayuan Ya Bude Sabon Babin Shiga Wasanni Na Zamani

Yadda Wani Tsohon A Kauyen Liujiayuan Ya Bude Sabon Babin Shiga Wasanni Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.