ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudummawar Mata A Harkar Samar Da Tsaro A Nijeriya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
Gudummawar Mata

A yayin da muke yaba wa rundunonin tsaro ta bangaren gwamnati da na masu zaman kansu da suke aiki babbu kakkautawa don samar mana da cikakken tsaro tare da tabbatar da al’umma basu fuskantar wata matsala a sassan Nijeriya, muna yaba wa kungiyar maharba mata ta Jihar Taraba, wadda a ‘yan kwanakin nan ta nuna cewa, yaki da rashin tsaro ba abu ba ne da za a kebewa maza kawai suma mata na iya bayar da nasu gudunmawar.

Wadannan jaruman matan sun shiga kafada da kafada wajen yaki da ‘yan ta’addan da suka addabi al’umma jihar a ‘yan shekarun nan.

A Nijeriya tarihi ya nuna cewa, mata sun bayar da gaggarumar gudummawa wajen tabbatar da cikakken tsaro a cikin al’umma kuma bai kamata a manta gaba daya da hakan ba. Haka kuma mata na ci gaba da kasancewa a kan gaba a rundunonin tsaron Nijeriya, kamar Rundunar Sojin Nijeriya, ‘Yan sanda ‘Civil Defense’ da sauran rundunonin tsaro masu zaman kansu wajen yaki da matsalar tsaro a sassan kasar nan.

ADVERTISEMENT

A kasar da mata suka kai fiye da mutum miliyan 200 wannan ba zai taba zama abin mamaki ga kowa ba. Tabbas rashin sanya mata a cikin tsarin jami’an tsaron kasa ba zai haifar da da mai ido ba musamman ganin yadda matsalar tsaro take kara karuwa.

A ‘yan kwanakin nan wasu jaruman mata suka hada hannu da takwarorin su maza a Jihar Taraba, don su yaki ayyukan ta’addanci da ta addabi yankunan, a halin yanzu zawarawan da ‘yan mata suna gangamin shiga wannan kungiyar, wannan wani lamari ne da ya kamata a yaba a kuma karfafa. Hare-haren da ake kai wa mata da yara kanana ya tilastawa matan shiga wannan kungiyar tare da daukar makamai don kare al’ummar su.

LABARAI MASU NASABA

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

Idan za a iya tunawa a watan Janairu na shekarar 2022 ne aka tura akalla sojoji mata fiye da 300 don aiki tare da sauran jami’an tsaron wajen yaki da ayyukan ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane da sauran ayyukan ta’addanci a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja a daidai lokacin lokacin da lamarin ayyukan ta’addancin ya ta’azzara.

Hakanan ma a shekarar 2018, shugaban rundunar sojojin Nijeriya na wancan lokacin Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai, ya karfafa mata yayin da ya kafa wata runduna ta musamman a yankin Afirika ta yamma.
Shigar da mata cikin tsarin harkar samar da tsaro a dukkan matakai a Nijeriya abu ne da ya karbu a sassan duniya kuma bai kamata a ce Nijeriya bata shiga sahu ba.

A lokacin da Buratai ya kafa Rundunar Sojoji Mata na Sojojin Nijeriya, ya bayyana cewa, “Za a ba rundunar dukkan goyon bayan da take bukata na shigar da mata a tsaron don su bayar da gudummawarsu na tabbatar da cikakkiyar tsaro a kasar mu.

Tarihi ya nuna irin nasarorin da mata suka samu a kokrin samar da tsaro a sassa daban-daban a Nijeriya. A wannan fannin tabass za mu iya tuna kungiyar tsaro da ake kira ‘Female amazons’ ta Jihar Filato, wadanda suke saukowa daga kan tsaunuka don kare al’ummar su daga hare-hare, haka kuma muna iya tunawa da Sarauniya Amina wadda ta jagoranci dakarun mahaifinta a yake-yake da aka yi wajen kare daular Zazzau.

Akwai kuma wasu mayaka mata a wasu kasashen yankin Afirka ta Yamma da suka hada da kasar Dahomey, a wanncan lokacin ana kiran matan da sunan “Black Sparta.” Sun yi kokarin fafatawa ba tare da tsoro ba wajen tunkarar yakin da ake yi da safarar mutane da sunan bayi.

Jarumai mata a sassan duniya sun nuna cewa, mata na iya bayar da gudummawar su wajen yaki da matsalar tsaro tare da tabbatar da tsaro a cikin al’umma.
An kuma samu rahotannin zaratan sojoji mata da suka fafata a cikin dakarun kasar ‘Kurdish Peshmerga’ a watan Yuni na shekarar 2014, inda suka shiga sahun dakarun da suka yaki don kwato garin Mosul na kasar Irak daga hannun kungiyar nan ta ‘yan ta’adda ta ISIS. Haka kuma bayan shekara 2 sun kuma kara fafatawa a karkashin dakaru mata fiye da 1,000 inda suka ceto garin Kirkuk da wasu rijiyoyin mai na kasar Irak daga hannun ‘yan ta’addar kungiyar ISIS.

A al’adance ana ganin mata a mastayin masu rauni da ba za su iya tafiya kafada da kafada da takwarorinsu maza ba amma a halihn yanzu al’amurra sun canza, yanzu mata na hada hannu da maza wajen dukkan ayyukan samar da tsaro a cikin al’umma.

A jawabin Gwamnan Jihar Kaduna a yayin da yake karbar matan da aka turo don yin aikin samar da tsrao a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja, ya ce, “tabbas duk abin da namiji zai iya yi mace ma za ta iya yin fiye da haka. Mun yi imanin matan Jihar Kaduna suna iya gabatar da ayyuka kamar maza suna kuma da kwarewar da ake bukata, za mu baku dukkan gudummawar da ake bukata don ku samu nasarar da ake bukata a wanan lokacin, muna alfahari da kasancewa ku, zuwan ku zai karfafa sauran matan jihar shiga aikin soja,” In ji shi.

Ba zamu manta da ‘Flying Officer Tolulope Arotile, da gudummawarta ga yaki da ta’addanci a yankin arewacin Nijeriya ba. Ita ce mace ta farko da ta fara tuka jirgin saman yaki na rundunar sojojin sama a Nijeriya. Nijeriya ta yi alhinin rasuwarta a shekarar 2021.

Haka kuma muna tuna mata da dama da suka rasa rayukansu ko suka bace a yayin da suke bautawa kasar haihuwarsu. Za a ci gaba da tunawa da su har abada.

Gudummawar Mata
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

MASU ALAKA

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta
Manyan Labarai

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu
Manyan Labarai

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
Next Post
Yadda Wani Tsohon A Kauyen Liujiayuan Ya Bude Sabon Babin Shiga Wasanni Na Zamani

Yadda Wani Tsohon A Kauyen Liujiayuan Ya Bude Sabon Babin Shiga Wasanni Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

Sabon Rikici Ya Kunno Kai A NDC, An Buƙaci INEC Ta Soke Rijistarta

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

An Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram, Wasu Na Can Riƙe Wurinsu

June 8, 2026
Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.