• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Likitoci Sinawa Ke Tallafawa Masu Larurar Ido A Ghana

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Likitoci Sinawa Ke Tallafawa Masu Larurar Ido A Ghana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda Bahaushe kan ce “Lafiya Uwar Jiki”, babu mai fushi da ke, mun sani cewa daya daga muhimman fannonin kare lafiyar dan adam shi ne fannin lafiyar ido. Ga wadanda suke fuskantar larurar gani ko ciwon ido, su kan shiga wani yanayi mawuyaci, tare da fafutukar neman magani.

To sai dai a kasar Ghana dake yammacin nahiyar Afirka, masu irin wannan larura sun yi gam-da-katar, domin kuwa, tun daga watan Nuwambar bara, wata tawagar likitocin kasar Sin da aka aike kasar, tana gudanar da tiyata kyauta, ga masu fama da matsalolin ido, ciki har da masu fama da cutar yanar ido ko “cataracts” a Turance.

  • An Saurari Bayani Game Da Yanayin Yaki Da Cutar COVID-19 Na Kasar Sin

Al’ummun kasar Ghana da dama, sun ci gajiya daga hidimomin kula da idanu da tawagar likitocin na kasar Sin ke bayarwa. Tun daga wancan lokaci zuwa yanzu. Jama’a na samun damar a duba idanunsu, tare da ba su magani, ko ma yi musu aiki idan ta kama, a cibiyar da likitocin na Sin ke aiki, wadda take asabitin ido na LEKMA, a birin Accra, fadar mulkin kasar.

Ga masu karamin karfi dake fama da yanar ido, abu ne mai wahala su iya samun magani, duba da cewa, aikin wannan cuta na da tsada, don haka wasu daga cikinsu, su kan hakura da yanayin da suke ciki, har ta kai ga sun rasa ganin su baki daya. Amma zuwan wannan tawaga ta likitocin ido daga kasar Sin, ya farfado da fatansu na samun lafiya, matakin da ke matukar samun yabo daga dukkanin al’ummar kasar baki daya.

Idan za mu iya tunawa, tun a baya, mahukuntan kasar Sin sun sha alkawarta tallafawa kasashe masu tasowa ta fannin kiwon lafiya, kuma karkashin manufofin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka na FOCAC, Sin ta aiwatar da matakai daban daban, na agazawa kasashen Afirka da kayan aiki, da tallafin kwararru, wanda tuni kasashen nahiyar da dama suka ci gajiyar hakan. La’akari da haka, ma iya cewa, Sin tana cika alkawura da ta dauka ga kawayenta na Afirka, kuma kwalliya na biyan kudin sabulu, game yaukakar alakar Sin da abokanta na nahiyar Afirka, da ma burin kasar ta Sin, na samar da al’ummar duniya mai makomar bai daya daga dukkanin fannoni. (Saminu Hassan)

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Motoci Masu Amfani Da Sabbin Makamashi Da Sin Ta Fitar Zuwa Ketare Ya Ci Gaba Da Karuwa A Bara

Next Post

2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

Related

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

17 hours ago
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

18 hours ago
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci
Daga Birnin Sin

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

19 hours ago
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

20 hours ago
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

21 hours ago
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

23 hours ago
Next Post
2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

LABARAI MASU NASABA

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

September 2, 2025
NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

September 2, 2025
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.