ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Muhimman Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Kafin Ranar Zabe

by Sulaiman
4 years ago
Zabe

Yanzu dai kwanaki 9 kacal su ka rage a yi zaɓen shugaban ƙasa. Akwai muhimman batutuwa 10 da ya kamata a sani dangane da wannan zaɓe.

 

Mutum miliyan 93.5 su ka yi rajistar zaɓe. Sai dai ba lallai dukkan su ne za su yi zaɓe ba.

ADVERTISEMENT
  • Na Bai Wa Bankuna Umarnin Wadata Mutane Da Takardun N200 – Emefiele

Zaɓen Nijeriya ya kai kwatankwacin zaɓen sauran ƙasashen Afrika ta Yamma baki ɗaya yawa, idan da a ce za su haɗu su yi zaɓe a rana ɗaya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

INEC ta buga ƙuri’u miliyan 187 don zaɓen shugaban ƙasa. Za a yi amfani da rabin su a lokacin zaɓen 25 ga Fabrairu. Idan ta kama sai an yi zaɓen raba-gardama, wato zagaye na biyu, sai a yi amfani da sauran rabin ƙuri’un kenan.

 

Jam’iyyu 18 ne su ka fitar da ‘yan takarar shugaban ƙasa a zaɓen ranar 25 ga Fabrairu.

 

Idan ta kama a yi zaɓen raba-gardama, wato zagaye na biyu yayin da zaɓen shugaban ƙasa bai fitar da wanda ya yi nasara ba, to INEC za ta shirya zaɓen a cikin kwanaki 21.

 

Idan kuma ba za a yi zaɓen raba-gardama ba, kuma wani ɗan takarar shugaban ƙasa bai kai ƙara kotu ba, to INEC za ta ƙone sauran ƙarin takardun zaɓe miliyan 93.5 da ta buga.

 

Akwai rumfunan zaɓe 176,846 da za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa. Amma yanzu sun koma 176, 606, saboda INEC ta sanar cewa ba za a yi zaɓe a rumfuna 240 cikin jihohi 28 da FCT Abuja ba.

 

9. Adadin ejan-ejan ɗin da Jam’iyyu 18 za su tura wurin zaɓe ya kai 1,642,386. A cikin su 1,574,301 ejan ne a rumfunan zaɓe, wato ‘polling egents’. Sai 68,088 kuma ejan-ejan ne masu sa-ido wurin tattara sakamakon zaɓe, wato ‘collation egents’.

 

Jihohin Taraba da Imo ne ke da mafi yawan rumfunan da ba za a yi zaɓe a cikin su ba. Yayin da Taraba ke da rumfuna 34, Jihar Imo kuwa har 38.

 

INEC ta ce ta rigaya ta bayar da katin shaidar ejan ga wakilan jam’iyyu a wurin zaɓe da wurin tattara sakamakon zaɓe. Saboda haka ba ta yarda mutum biyu su fito su ce jam’iyyya ɗaya su ke wakilta ba. Ejan ɗaya kaɗai INEC ta sani. Wanda ya yi karambani ko gangancin yi wa INEC shisshigi, za a damƙe shi ya fuskanci hukunci.

Zabe
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Zabe
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Fasto Ya Mutu A Kokarin Yin Azumin Kwana 40

Fasto Ya Mutu A Kokarin Yin Azumin Kwana 40

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.