• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Goyon Bayan Tsarin Zabe Ne Ba Dan Takara Ba – Amurka

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Zabe

Gwamnatin kasar Amurka ta bayyana cewa ba ta goyon bayan duk wani dan takara ko jam’iyya a zaben ranar 25 ga watan Fabrairun da ranar 11 ga watan Maris a Nijeriya.

Mataimakiyar sakatariyar harkokin wajen Amurka mai kula da harkokin Afirka, Molly Phee ita ta bayyana hakan yayin da ta kai ziyara ga shugabannin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Abuja.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 2 Hukunci Kisa Kan Kashe Ma’aurata A Ondo

Ta ce damuwar Amurka a matsayinta na mai habaka dimokuradiyya shi ne, karfafa gudanar da zabe cikin nasara wanda zai kasance sahihi kuma mai cike da zaman lafiya da lumana.

Phee ta ce: “Tun a shekarar 1999, Nijeriya ta ci gaba da yin gyare-gyare wajen tabbatar da tsarin dimokuradiyya. Kuma a yanzu, a karkashin jagorancin shugaban hukumar INEC tare da tawagarsa, dukkan ‘yan Nijeriya za su iya amincewa da sahihancin zabe mai zuwa.

“Ina so in jaddada mahimmancin gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali, kuma ina so in jaddada cewa kowane dan kasa, kowane mai ruwa da tsaki, duk jam’iyyar da ke cikin zabe na da hakki kafin zabe, lokacin yakin neman zabe, lokacin zabe da kuma bayan zabe kasancewa cikin zaman lafiya da lumana. Yana da matukar muhimmanci, domin kalubale ne da muka fuskanta a kasarmu.”

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, yayin da yake mayar da martani ya nanata cewa hukumar ba ta siyasa ba ce, kuma ba ta da dan takara da take mara wa baya.

Ya kuma ba da tabbacin hukumar zabe za ta tabbatar da zabin da ‘yan Nijeriya suka yi a zaben.

Yakubu ya kara da cewa: “Kamar dai kasar Amurka, hukumar ba jam’iyyar siyasa ba ce. Ba mu da ‘yan takara kuma za mu mayar da hankali ne kawai kan tsarin.

“Zabi na mutanen Nijeriya ne, kuma hukumar za ta tabbatar da zabin da ‘yan Nijeriya suka yi. Mun himmatu wajen tabbatar da sahihin zabe a 2023.

“A zahirin gaskiya, Amurka tana sha’awar dimokuradiyyar Nijeriya, ita ma Nijeriya tana sha’awar dimokuradiyyar Amurka. Na fadi wannan a Washington ga wadanda ba su ji ni ba. Ina so in sake maimaitawa. Idan Amurka ce babbar dimokuradiyyar shugaban kasa a duniya, wace kasa ce ta biyu mafi girman dimokuradiyya a duniya? A zahiri Nijeriya ce.

“Bisa kiyasin yawan al’ummar Nijeriya nan da shekaru biyu masu zuwa, wa ya san mu ma za mu iya zarce Amurka gaba daya wajen dimokuradiyya mafi girma a duniya. Don haka, muna sha’awar tabbatar da karfafa dimokuradiyyarmu. Babu wani tsarin gwamnati da ya fi tsarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025
Next Post
Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

LABARAI MASU NASABA

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.