• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Goyon Bayan Tsarin Zabe Ne Ba Dan Takara Ba – Amurka

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai, Tambarin Dimokuradiyya
0
Muna Goyon Bayan Tsarin Zabe Ne Ba Dan Takara Ba – Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin kasar Amurka ta bayyana cewa ba ta goyon bayan duk wani dan takara ko jam’iyya a zaben ranar 25 ga watan Fabrairun da ranar 11 ga watan Maris a Nijeriya.

Mataimakiyar sakatariyar harkokin wajen Amurka mai kula da harkokin Afirka, Molly Phee ita ta bayyana hakan yayin da ta kai ziyara ga shugabannin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Abuja.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 2 Hukunci Kisa Kan Kashe Ma’aurata A Ondo

Ta ce damuwar Amurka a matsayinta na mai habaka dimokuradiyya shi ne, karfafa gudanar da zabe cikin nasara wanda zai kasance sahihi kuma mai cike da zaman lafiya da lumana.

Phee ta ce: “Tun a shekarar 1999, Nijeriya ta ci gaba da yin gyare-gyare wajen tabbatar da tsarin dimokuradiyya. Kuma a yanzu, a karkashin jagorancin shugaban hukumar INEC tare da tawagarsa, dukkan ‘yan Nijeriya za su iya amincewa da sahihancin zabe mai zuwa.

“Ina so in jaddada mahimmancin gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali, kuma ina so in jaddada cewa kowane dan kasa, kowane mai ruwa da tsaki, duk jam’iyyar da ke cikin zabe na da hakki kafin zabe, lokacin yakin neman zabe, lokacin zabe da kuma bayan zabe kasancewa cikin zaman lafiya da lumana. Yana da matukar muhimmanci, domin kalubale ne da muka fuskanta a kasarmu.”

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, yayin da yake mayar da martani ya nanata cewa hukumar ba ta siyasa ba ce, kuma ba ta da dan takara da take mara wa baya.

Ya kuma ba da tabbacin hukumar zabe za ta tabbatar da zabin da ‘yan Nijeriya suka yi a zaben.

Yakubu ya kara da cewa: “Kamar dai kasar Amurka, hukumar ba jam’iyyar siyasa ba ce. Ba mu da ‘yan takara kuma za mu mayar da hankali ne kawai kan tsarin.

“Zabi na mutanen Nijeriya ne, kuma hukumar za ta tabbatar da zabin da ‘yan Nijeriya suka yi. Mun himmatu wajen tabbatar da sahihin zabe a 2023.

“A zahirin gaskiya, Amurka tana sha’awar dimokuradiyyar Nijeriya, ita ma Nijeriya tana sha’awar dimokuradiyyar Amurka. Na fadi wannan a Washington ga wadanda ba su ji ni ba. Ina so in sake maimaitawa. Idan Amurka ce babbar dimokuradiyyar shugaban kasa a duniya, wace kasa ce ta biyu mafi girman dimokuradiyya a duniya? A zahiri Nijeriya ce.

“Bisa kiyasin yawan al’ummar Nijeriya nan da shekaru biyu masu zuwa, wa ya san mu ma za mu iya zarce Amurka gaba daya wajen dimokuradiyya mafi girma a duniya. Don haka, muna sha’awar tabbatar da karfafa dimokuradiyyarmu. Babu wani tsarin gwamnati da ya fi tsarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaNijeriyaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dakatar Da Binani: Mazaba Ba Ta Da Ikon Dakatar Da Mutum Daga Jam’iyya -Sakataren APC

Next Post

Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

13 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 day ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

1 day ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 day ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

LABARAI MASU NASABA

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.