ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Goyon Bayan Tsarin Zabe Ne Ba Dan Takara Ba – Amurka

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Zabe

Gwamnatin kasar Amurka ta bayyana cewa ba ta goyon bayan duk wani dan takara ko jam’iyya a zaben ranar 25 ga watan Fabrairun da ranar 11 ga watan Maris a Nijeriya.

Mataimakiyar sakatariyar harkokin wajen Amurka mai kula da harkokin Afirka, Molly Phee ita ta bayyana hakan yayin da ta kai ziyara ga shugabannin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Abuja.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 2 Hukunci Kisa Kan Kashe Ma’aurata A Ondo

Ta ce damuwar Amurka a matsayinta na mai habaka dimokuradiyya shi ne, karfafa gudanar da zabe cikin nasara wanda zai kasance sahihi kuma mai cike da zaman lafiya da lumana.

ADVERTISEMENT

Phee ta ce: “Tun a shekarar 1999, Nijeriya ta ci gaba da yin gyare-gyare wajen tabbatar da tsarin dimokuradiyya. Kuma a yanzu, a karkashin jagorancin shugaban hukumar INEC tare da tawagarsa, dukkan ‘yan Nijeriya za su iya amincewa da sahihancin zabe mai zuwa.

“Ina so in jaddada mahimmancin gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali, kuma ina so in jaddada cewa kowane dan kasa, kowane mai ruwa da tsaki, duk jam’iyyar da ke cikin zabe na da hakki kafin zabe, lokacin yakin neman zabe, lokacin zabe da kuma bayan zabe kasancewa cikin zaman lafiya da lumana. Yana da matukar muhimmanci, domin kalubale ne da muka fuskanta a kasarmu.”

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, yayin da yake mayar da martani ya nanata cewa hukumar ba ta siyasa ba ce, kuma ba ta da dan takara da take mara wa baya.

Ya kuma ba da tabbacin hukumar zabe za ta tabbatar da zabin da ‘yan Nijeriya suka yi a zaben.

Yakubu ya kara da cewa: “Kamar dai kasar Amurka, hukumar ba jam’iyyar siyasa ba ce. Ba mu da ‘yan takara kuma za mu mayar da hankali ne kawai kan tsarin.

“Zabi na mutanen Nijeriya ne, kuma hukumar za ta tabbatar da zabin da ‘yan Nijeriya suka yi. Mun himmatu wajen tabbatar da sahihin zabe a 2023.

“A zahirin gaskiya, Amurka tana sha’awar dimokuradiyyar Nijeriya, ita ma Nijeriya tana sha’awar dimokuradiyyar Amurka. Na fadi wannan a Washington ga wadanda ba su ji ni ba. Ina so in sake maimaitawa. Idan Amurka ce babbar dimokuradiyyar shugaban kasa a duniya, wace kasa ce ta biyu mafi girman dimokuradiyya a duniya? A zahiri Nijeriya ce.

“Bisa kiyasin yawan al’ummar Nijeriya nan da shekaru biyu masu zuwa, wa ya san mu ma za mu iya zarce Amurka gaba daya wajen dimokuradiyya mafi girma a duniya. Don haka, muna sha’awar tabbatar da karfafa dimokuradiyyarmu. Babu wani tsarin gwamnati da ya fi tsarin.

Zabe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.