• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Goyon Bayan Tsarin Zabe Ne Ba Dan Takara Ba – Amurka

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai, Tambarin Dimokuradiyya
0
Muna Goyon Bayan Tsarin Zabe Ne Ba Dan Takara Ba – Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin kasar Amurka ta bayyana cewa ba ta goyon bayan duk wani dan takara ko jam’iyya a zaben ranar 25 ga watan Fabrairun da ranar 11 ga watan Maris a Nijeriya.

Mataimakiyar sakatariyar harkokin wajen Amurka mai kula da harkokin Afirka, Molly Phee ita ta bayyana hakan yayin da ta kai ziyara ga shugabannin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Abuja.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 2 Hukunci Kisa Kan Kashe Ma’aurata A Ondo

Ta ce damuwar Amurka a matsayinta na mai habaka dimokuradiyya shi ne, karfafa gudanar da zabe cikin nasara wanda zai kasance sahihi kuma mai cike da zaman lafiya da lumana.

Phee ta ce: “Tun a shekarar 1999, Nijeriya ta ci gaba da yin gyare-gyare wajen tabbatar da tsarin dimokuradiyya. Kuma a yanzu, a karkashin jagorancin shugaban hukumar INEC tare da tawagarsa, dukkan ‘yan Nijeriya za su iya amincewa da sahihancin zabe mai zuwa.

“Ina so in jaddada mahimmancin gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali, kuma ina so in jaddada cewa kowane dan kasa, kowane mai ruwa da tsaki, duk jam’iyyar da ke cikin zabe na da hakki kafin zabe, lokacin yakin neman zabe, lokacin zabe da kuma bayan zabe kasancewa cikin zaman lafiya da lumana. Yana da matukar muhimmanci, domin kalubale ne da muka fuskanta a kasarmu.”

Labarai Masu Nasaba

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, yayin da yake mayar da martani ya nanata cewa hukumar ba ta siyasa ba ce, kuma ba ta da dan takara da take mara wa baya.

Ya kuma ba da tabbacin hukumar zabe za ta tabbatar da zabin da ‘yan Nijeriya suka yi a zaben.

Yakubu ya kara da cewa: “Kamar dai kasar Amurka, hukumar ba jam’iyyar siyasa ba ce. Ba mu da ‘yan takara kuma za mu mayar da hankali ne kawai kan tsarin.

“Zabi na mutanen Nijeriya ne, kuma hukumar za ta tabbatar da zabin da ‘yan Nijeriya suka yi. Mun himmatu wajen tabbatar da sahihin zabe a 2023.

“A zahirin gaskiya, Amurka tana sha’awar dimokuradiyyar Nijeriya, ita ma Nijeriya tana sha’awar dimokuradiyyar Amurka. Na fadi wannan a Washington ga wadanda ba su ji ni ba. Ina so in sake maimaitawa. Idan Amurka ce babbar dimokuradiyyar shugaban kasa a duniya, wace kasa ce ta biyu mafi girman dimokuradiyya a duniya? A zahiri Nijeriya ce.

“Bisa kiyasin yawan al’ummar Nijeriya nan da shekaru biyu masu zuwa, wa ya san mu ma za mu iya zarce Amurka gaba daya wajen dimokuradiyya mafi girma a duniya. Don haka, muna sha’awar tabbatar da karfafa dimokuradiyyarmu. Babu wani tsarin gwamnati da ya fi tsarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaNijeriyaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dakatar Da Binani: Mazaba Ba Ta Da Ikon Dakatar Da Mutum Daga Jam’iyya -Sakataren APC

Next Post

Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

Related

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

7 hours ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

8 hours ago
Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari

8 hours ago
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura
Manyan Labarai

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

8 hours ago
Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina
Manyan Labarai

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

9 hours ago
HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
Hotuna

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

11 hours ago
Next Post
Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

LABARAI MASU NASABA

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

July 15, 2025
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.