• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tawagar Jami’an Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa NIS mai Mutum Takwas ta kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu hedikwatar Hukumar Kula da Kan iyakokin Turai FRONTEX a makon da ya gabata don tattaunawa da Jami’an hukumar kan harkokin tsaro da kula da bakin haure.

NIS
Hoton mahalarta taron

Tawagar wacce mataimakin Kwanturola Janar, Muhammad Aminu Muhammad mni, mai kula da sashes tsaron iyakokin Nijeriya ya jagoranta, ta samu tarba daga manyan jami’an hukumar FRONTEX karkashin jagorancin Mista Iain Galea a hedkwatar FRONTEX da ke Warsaw a kasar Poland.
A jawabinta na maraba, shugabar riko ta FRONTEX Aija Kalnaja ta bayyana cewa hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya (NIS) aminiyar hukumarsu ce ta FRONTEX a fannin tsaro da kula da bakin haure.

NIS
Lokacin da ake zaman tattaunawar

Kalnaja ta jaddada cewa dangantakar da ke tsakanin hukumar FRONTEX da NIS ta samo asali ce tun a shekarar 2012 lokacin da hukumomin biyu suka shiga cikin wani tsari na aiki kan tsaro kan iyaka da kula da bakin haure.
Ta kuma sake gabatar da bukatar sake inganta hadin gwiwa daga hukumomin kan iyakoki don ci gaba da yaki da laifuffukan fasa kwari musamman masu safarar Mutane da haramtattun kaya.

  • Yadda Aka Yi Wa Kwanturola Janar Na NIS Ado Da Sabon Muƙaminsa

“Ina fatan dukkan hukumomin biyu za su yi amfani da cin moriyar wannan taron don sake nazarin tsarin Ayyuka don ganin ko akwai wuraren da za a iya sake ingantawa su yi daidai da tsarin zamani” in ji ta.

NIS
Zauren tattaunawar

A jawabin godiyarsa, shugaban tawagar NIS kuma shugaban sashen kula da kan iyakoki, DCG Aminu Muhammad ya bayyana jin dadinsa da irin tarbar da aka yi wa tawagarsa, inda Ya sake nanata kwakkwaran kudurin NIS na samar da ingantacciyar hadin gwiwa da hukumomin tsaro na kan iyakoki, kamar irin su FRONTEX sannan kuma ya yi kira ga bangarori biyun su tattauna manyan kalubalen bangarorin a yayin gudanar da taron.

Labarai Masu Nasaba

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

DCG Muhammad ya kuma jaddada bukatar da ke akwai ta ganin kasashen Turai da sauran kasashen da suka ci gaba sun yi bitar shirye-shirye masu dorewa na hadin kai da hukumomi domin shawo kan matsalolin abubuwan da suke jawo yin kaura a wannan zamani fiye da kafa shinge kan iyakoki don shawo kan kwararowar bakin haure.

NIS
Ya nusar da cewa kudaden da ake kashewa na gina manyan shinge kan iyakoki ba zai samar da fa’ida mai dorewa ba idan yanayin rayuwar jama’a a kasashe masu tasowa ya kasance cikin mawuyacin hali.

Tun da farko, wanda ya shirya tafiyar zuwa hukumar FRONTEX, wakilin kasar a FIIAPP, shiri mai kula da yaki da fataucin mutane da safarar bakin haure a Nijeriya (A-TIPSOM), Mista Rafael Molina ya bayyana cewa ofishinsa ya yanke shawarar tsara tafiyar ce da nufin habaka hadin gwiwa tsakanin FRONTEX da NIS don yaki da balaguro mara ka’ida kuma mai hadari.

  • https://immigration.gov.ng/

An dauki lokaci mai tsawo ana tattauna muhimman al’amura kamar tsarin Hijira da aiki da na’urar tantance bayanan matafiya ta (MIDAS), da kuma tsarin Cibiyar Nazarin Hijira ta NIS da sauransu.

 

Wasu daga cikin muhimman abubuwan da suka fi daukar hankali a taron sun hada da nuna kwarin gwiwa wajen inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin biyu wajen yaki da hijira ba bisa ka’ida ba tare da bayar da tabbaci mai karfi na inganta ayyukan samar da bayanai a tsakanin hukumomin biyu.

NIS

Bayan kammala Taron, tawagar jami’an NIS sun ziyarci ofishin jakadancin Nijeriya inda suka samu tarba ta musammam daga Ambasada Manjo Janar mai ritaya, Christian C Ugwu, wakilin Nijeriya a kasar Poland da abokan aikinsa.
Tuni dai tawagar hukumar ta NIS ta dawo gida lami da lafiya, inda ta sauka a Abuja Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kaduna Ta Sake Sallamar Malaman Makaranta 2,357 Daga Aiki

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Hakimi Da Dansa A Bauchi

Related

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
Labarai

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

2 hours ago
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
Labarai

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

2 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

3 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa
Labarai

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

5 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

7 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Hakimi Da Dansa A Bauchi

'Yan Bindiga Sun Sace Hakimi Da Dansa A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

June 25, 2025
Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.