ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki

by Sulaiman
4 years ago
NIS

Tawagar Jami’an Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa NIS mai Mutum Takwas ta kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu hedikwatar Hukumar Kula da Kan iyakokin Turai FRONTEX a makon da ya gabata don tattaunawa da Jami’an hukumar kan harkokin tsaro da kula da bakin haure.

NIS
Hoton mahalarta taron

Tawagar wacce mataimakin Kwanturola Janar, Muhammad Aminu Muhammad mni, mai kula da sashes tsaron iyakokin Nijeriya ya jagoranta, ta samu tarba daga manyan jami’an hukumar FRONTEX karkashin jagorancin Mista Iain Galea a hedkwatar FRONTEX da ke Warsaw a kasar Poland.
A jawabinta na maraba, shugabar riko ta FRONTEX Aija Kalnaja ta bayyana cewa hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya (NIS) aminiyar hukumarsu ce ta FRONTEX a fannin tsaro da kula da bakin haure.

NIS
Lokacin da ake zaman tattaunawar

Kalnaja ta jaddada cewa dangantakar da ke tsakanin hukumar FRONTEX da NIS ta samo asali ce tun a shekarar 2012 lokacin da hukumomin biyu suka shiga cikin wani tsari na aiki kan tsaro kan iyaka da kula da bakin haure.
Ta kuma sake gabatar da bukatar sake inganta hadin gwiwa daga hukumomin kan iyakoki don ci gaba da yaki da laifuffukan fasa kwari musamman masu safarar Mutane da haramtattun kaya.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Aka Yi Wa Kwanturola Janar Na NIS Ado Da Sabon Muƙaminsa

“Ina fatan dukkan hukumomin biyu za su yi amfani da cin moriyar wannan taron don sake nazarin tsarin Ayyuka don ganin ko akwai wuraren da za a iya sake ingantawa su yi daidai da tsarin zamani” in ji ta.

NIS
Zauren tattaunawar

A jawabin godiyarsa, shugaban tawagar NIS kuma shugaban sashen kula da kan iyakoki, DCG Aminu Muhammad ya bayyana jin dadinsa da irin tarbar da aka yi wa tawagarsa, inda Ya sake nanata kwakkwaran kudurin NIS na samar da ingantacciyar hadin gwiwa da hukumomin tsaro na kan iyakoki, kamar irin su FRONTEX sannan kuma ya yi kira ga bangarori biyun su tattauna manyan kalubalen bangarorin a yayin gudanar da taron.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

DCG Muhammad ya kuma jaddada bukatar da ke akwai ta ganin kasashen Turai da sauran kasashen da suka ci gaba sun yi bitar shirye-shirye masu dorewa na hadin kai da hukumomi domin shawo kan matsalolin abubuwan da suke jawo yin kaura a wannan zamani fiye da kafa shinge kan iyakoki don shawo kan kwararowar bakin haure.

NIS
Ya nusar da cewa kudaden da ake kashewa na gina manyan shinge kan iyakoki ba zai samar da fa’ida mai dorewa ba idan yanayin rayuwar jama’a a kasashe masu tasowa ya kasance cikin mawuyacin hali.

Tun da farko, wanda ya shirya tafiyar zuwa hukumar FRONTEX, wakilin kasar a FIIAPP, shiri mai kula da yaki da fataucin mutane da safarar bakin haure a Nijeriya (A-TIPSOM), Mista Rafael Molina ya bayyana cewa ofishinsa ya yanke shawarar tsara tafiyar ce da nufin habaka hadin gwiwa tsakanin FRONTEX da NIS don yaki da balaguro mara ka’ida kuma mai hadari.

  • https://immigration.gov.ng/

An dauki lokaci mai tsawo ana tattauna muhimman al’amura kamar tsarin Hijira da aiki da na’urar tantance bayanan matafiya ta (MIDAS), da kuma tsarin Cibiyar Nazarin Hijira ta NIS da sauransu.

 

Wasu daga cikin muhimman abubuwan da suka fi daukar hankali a taron sun hada da nuna kwarin gwiwa wajen inganta hadin gwiwa tsakanin hukumomin biyu wajen yaki da hijira ba bisa ka’ida ba tare da bayar da tabbaci mai karfi na inganta ayyukan samar da bayanai a tsakanin hukumomin biyu.

NIS

Bayan kammala Taron, tawagar jami’an NIS sun ziyarci ofishin jakadancin Nijeriya inda suka samu tarba ta musammam daga Ambasada Manjo Janar mai ritaya, Christian C Ugwu, wakilin Nijeriya a kasar Poland da abokan aikinsa.
Tuni dai tawagar hukumar ta NIS ta dawo gida lami da lafiya, inda ta sauka a Abuja Nijeriya.

NIS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Hakimi Da Dansa A Bauchi

'Yan Bindiga Sun Sace Hakimi Da Dansa A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.