• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: ‘Yan Daba Sun Sace Na’urar BVAS 8 A Delta Da Katsina

by Khalid Idris Doya
3 years ago
BVAS

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta ce, ‘yan daba sun tarwatsa aikin zabe a Jihar Delta da Katsina, inda suka yi awon gaba da na’urar tantance masu zabe BVAS har guda takwas.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan a hirarsa da manema labarai a ranar Asabar.

  • Zaben 2023: Atiku Ya Lashe Mazabar Shugaban Majalisar Dattawa A Yobe
  • Zaben 2023: Peter Obi Ya Lashe Akwatin Mazabarsa A Anambra

Ya yi bayanin cewa, a karamar hukumar Oshimili da ke jihar Delta, ‘yan daban sun kai hari rumfar zabe tare sannan suja sace na’urar BVAS guda biyu.

Kazalika, ya kara da cewa, a karamar hukumar Safana da ke Jihar Katsina, ‘yan daban sun hari kan wata cibiyar kada kuri’a tare da yin awon gaba da na’urar BVAS guda shida, amma a cewarsa jami’an tsaro sun samu nasarar kwato guda uku daga cikin shidan da aka sace.

Sannan, ya nuna takaicinsa cewa yanzu ‘yan daban siyasa sun koma harar mashin din BVAS.

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Mahmood ya cigaba da cewa aikin da ke rataye a kan hukumar shi ne tabbatar an gudanar da zaben ingatacce kuma sahihi wanda zai karbu.

A cewarsa, “A karamar hukumar Oshimili da ke jihar Delta, ‘yan daba sun farmaki rumfar zabe suka sace mashinan BVAS biyu a lokacin da aikin zaben ke gudana. Amma a bisa kokarinmu, nan da nan muka samu nasarar maye gurbin na’urorin da aka sace, tare da kara jibge jami’an tsaro kuma zabe ya cigaba da gudana.

“Sannan, a karamar hukumar Safana a jihar Katsina nan ma ‘yan daba sun farmaki rumfar zabenmu tare da sace BVAS 6. Amma mun samu nasarar kwato wasu, sannan an kara zuba jami’an tsaro kuma zaben ya cigaba da gudana kamar yadda aka tsara a wannan wurin.”

Ya ce, wannan shine karo na farko tun babban zaben 2011 da aka sanya zabe aka gudanar ba tare da dagewa ba.

“Mun tabbatar mun dage wajen cigaba da gudanar da abubuwan da suka dace. Zuwa yanzu mun samu nasarori sosai a yayin zaben nan kuma hanyar amfani da na’urar BVAS an samu aiki mai inganci.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
Firaministan Sin Ya Bukaci A Karfafa Ci Gaba Da Kuma Daidaita Farashin Kayayyaki

Firaministan Sin Ya Bukaci A Karfafa Ci Gaba Da Kuma Daidaita Farashin Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.