• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gayyaci Jakadan Burkina Faso Kan Kisan ‘Yan Nijeriya 16

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Burkina Faso

Gwamnatin Nijrtiya ta fara daukan kwakkwaran matakai domin bankado batutuwan da suke mamaye da kisan ‘yan Nijeriya 16 da suka yi niyyar zuwa ziyarar musulunci a Kaolack da ke kasar Senegal da ake zargin jami’an tsaron Burkina Faso ne suka kashe su.

 

Karamin ministan kula da harkokin cikin gida, Ambasada Zubairu Dada shi ne ya gayyaci jakadan na Burkina Faso Charge D’Affaires Passida Pascal Gouba a Nijeriya kan kisan gilla da aka yi tare da neman bayanin hakikanin abubuwan da suka faru wajen kisan ‘yan Nijeriya 16 da ake zargin sojojin Burkinabe da aikatawa.

  • Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

A cewarsa, Nijeriya ta damu sosai da wannan lamarin don haka tana bukatar cikin gaggawa a hanzarta samar da amsar tambayoyin da suke yi wa gwamnatin Burkina Faso, a cewar wata sanarwar da hadimin ministan a bangaren yada labarai, Ibrahim Aliyu ya fitar.

 

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Ministan ya nuna matukar kaduwarsa kan lamarin tare da misalta hakan da cewa abu ne da ba za a lamunta ba, kuma babu bukatar bata lokaci wajen samu gaskiyar abubuwan da suka faru cikin lamarin. Ya ce, ahlin mamatan su na ta yin tambayoyi daban-daban kuma su na bukatar a gaggauta yin bincike.

 

Ministan ya ce, Nijeriya ba za ta nade hannayenta haka nan tana kallo ana cin zarafi da kashe ‘yan kasarta a sassa daban-daban na duniya ba.

 

A nasa bangaren, ministan harkokin Burkina Faso a Nijeriya, Gouba, ya fara ne a jajanta wa iyalan mamatan tare da gwamnatin Nijeriya hadi da al’ummar kasar bisa abun da ya kira lamari na ban takaici da bakin ciki da ya faru. Ya ce, ya fahimci irin zafi da radadin da iyalan mamatan ke ji.

 

Ya ce, tunin gwamnatin Burkina Faso ta kaddamar da bincike domin ganowa da fito da asalin wadanda suka aiwatar da wannan kisan, ya kara da cewa a shirye suke su yi aiki tare da kwararrun tawaga daga Nijeriya domin gano hakikan abun da ya faru.

 

Daga bisani, Ambasada Dada ya kuma gana da wakilan kungiyar Darikar Tijaniyyah a karkashin jagorancin sakatare-janar na kungiyar Malam Muhammad Alkasim, inda ya masa bayani kan lamarin da ya faru tare da bayani kan ganawarsu da jakadan Burkina Fason.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Next Post
An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.