ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gayyaci Jakadan Burkina Faso Kan Kisan ‘Yan Nijeriya 16

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Burkina Faso

Gwamnatin Nijrtiya ta fara daukan kwakkwaran matakai domin bankado batutuwan da suke mamaye da kisan ‘yan Nijeriya 16 da suka yi niyyar zuwa ziyarar musulunci a Kaolack da ke kasar Senegal da ake zargin jami’an tsaron Burkina Faso ne suka kashe su.

 

Karamin ministan kula da harkokin cikin gida, Ambasada Zubairu Dada shi ne ya gayyaci jakadan na Burkina Faso Charge D’Affaires Passida Pascal Gouba a Nijeriya kan kisan gilla da aka yi tare da neman bayanin hakikanin abubuwan da suka faru wajen kisan ‘yan Nijeriya 16 da ake zargin sojojin Burkinabe da aikatawa.

ADVERTISEMENT
  • Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

A cewarsa, Nijeriya ta damu sosai da wannan lamarin don haka tana bukatar cikin gaggawa a hanzarta samar da amsar tambayoyin da suke yi wa gwamnatin Burkina Faso, a cewar wata sanarwar da hadimin ministan a bangaren yada labarai, Ibrahim Aliyu ya fitar.

 

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

Ministan ya nuna matukar kaduwarsa kan lamarin tare da misalta hakan da cewa abu ne da ba za a lamunta ba, kuma babu bukatar bata lokaci wajen samu gaskiyar abubuwan da suka faru cikin lamarin. Ya ce, ahlin mamatan su na ta yin tambayoyi daban-daban kuma su na bukatar a gaggauta yin bincike.

 

Ministan ya ce, Nijeriya ba za ta nade hannayenta haka nan tana kallo ana cin zarafi da kashe ‘yan kasarta a sassa daban-daban na duniya ba.

 

A nasa bangaren, ministan harkokin Burkina Faso a Nijeriya, Gouba, ya fara ne a jajanta wa iyalan mamatan tare da gwamnatin Nijeriya hadi da al’ummar kasar bisa abun da ya kira lamari na ban takaici da bakin ciki da ya faru. Ya ce, ya fahimci irin zafi da radadin da iyalan mamatan ke ji.

 

Ya ce, tunin gwamnatin Burkina Faso ta kaddamar da bincike domin ganowa da fito da asalin wadanda suka aiwatar da wannan kisan, ya kara da cewa a shirye suke su yi aiki tare da kwararrun tawaga daga Nijeriya domin gano hakikan abun da ya faru.

 

Daga bisani, Ambasada Dada ya kuma gana da wakilan kungiyar Darikar Tijaniyyah a karkashin jagorancin sakatare-janar na kungiyar Malam Muhammad Alkasim, inda ya masa bayani kan lamarin da ya faru tare da bayani kan ganawarsu da jakadan Burkina Fason.

Burkina Faso
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Next Post
An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

An Bude Taron Shekara-shekara Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.