• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Burin Kasar Sin Na Samun Bunkasar GDP Da Kashi 5% A Bana Zai Cika

by yahuzajere
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sharhi: Burin Kasar Sin Na Samun Bunkasar GDP Da Kashi 5% A Bana Zai Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu zantukan hikima kan ce “da icce mai kama ake kota”, tabbas haka ne, domin duk lokacin da wata kasa ta tasa wani buri a gaba, a kan duba a ga ko abin nan da take son cimmawa mai yiwuwa ne ko zai zama tamkar gurguwa da auren nesa bisa la’akari da matakai da ta dauka da kuma waiwayen abubuwan da ta gudanar a baya.

A bana, kasar Sin ta kudiri aniyar bunkasa tattalin arzikinta da a kalla kashi 5% (cikin dari), kamar yadda firmanistan kasar, Li Keqiang ya sanar a cikin rahoton ayyukan gwamnati da ya gabatar a taron wakilan majalisar jama’ar kasar, ranar 5 ga watan Maris din nan, baya ga kuma za ta samar da sabbin ayyukan yi miliyan 12, daidaita zaman kashe wando a birane da kashi 5.5, karin kashi 3% a mizanin farashin masu amfani da kayan masarufi.

Wannan kudiri da kasar Sin ta tsara cimmawa mai yiwuwa ne saboda dama kasar ba ta kwanta sai da zakara. Da farko abin da za a yi la’akari da shi, shi ne yadda kasar ta rika samun matsakaicin bunkasar tattalin arziki da mizanin 5.2% a cikin shekaru 5 da suka wuce, da kuma iya cin jarrabawar da bullar cutar COVID-19 ta yi mata, sai kuma wasu matakai da a halin yanzu ta dauka don cimma burin nata na samun ci gaba da kashi 5%.

Duk da cewa a shekarar 2022, kasar ba ta iya cimma kason da ta yi hankoron cimmawa a farko-farkon 2022 ba saboda wasu dalilan da suka shafi annobar COVID-19 da koma-bayan tattalin arzikin duniya, amma ta yi kokari da ta samu ci gaba da kashi 3% domin ba abu ne mai sauki a iya samun hakan ba a yanayi mai wuyar sha’ani da kan fado waka’an (ba-zata).

Har ila yau, matakan da kasar ta dauka domin tayar da komada daga COVID-19 a karshen bara da yadda kasar ta nuna kwazo a hada-hadar sarrafa kaya da cinikinsu da kuma ci gaban da ta samu na GDP a sulusin karshe na 2022 da kashi 2.9, duk sun zarce hasashen da aka yi na samun bunkasa, don haka wannan manuniya ce ga yiwuwar cimma burin kasar na bunkasa GDP da kashi 5%.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Bugu da kari, tun a farkon wannan shekarar, tattalin arzikin Sin ya samu ci gaba sakamakon kyawawan tsare-tsare da manufofi da gwamnatin kasa da ta kananan hukumomi suka dauka ta bangaren kudi, zuba jari, inganta yanayin kasuwanci da amfani da kayan masarufi da sauransu.

Bayanan da Hukumar Kididdiga ta Sin ta fitar a ranar 1 ga Maris, sun nuna an samu ci gaban sayen kayan da kasar Sin ta sarrafa a watan Fabrairu fiye da na watan Janairu da kashi 2.5. Wannan ya kara gaskata bayanan da aka fitar kwanan baya game da yadda farfadowar tattalin arzikin Sin ke samun ci gaba.

Don haka ma, galibin cibiyoyin da ke auna bunkasar tattalin arziki na duniya sun yi yakini game da habakar tattalin arzikin kasar Sin a bana, inda suka rika daga ma’aunin mizanin da suke hasashe a kai a kai. Misali, Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF), ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Sin zai bunkasa zuwa kashi 5.2% a bana. Haka nan mizanin Cibiyar Nomura Securities ya kyautata hasashen ci gaban zuwa kashi 5.3% daga kashi 4.8%. Ita ma Cibiyar Goldman Sachs ta yi hasashen abin zai kai 5.5%, sai kuma Morgan Stanley da hasashenta ya dara na kowa a cikinsu da ta ce tattalin arzikin na Sin zai bunkasa ne da kashi 5.7%.

Sakamakon dunkulewar tattalin arzikin duniya, ba shakka, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin zai taimakawa ci gaban duniya.

Misali a Afirka, kasar Sin ta zama gagarabadau wajen bunkasa manyan ayyukan more rayuwa a kasashe daban-daban da suka hada da hanyoyi, sufurin jiragen kasa, madatsun ruwa, filayen jiragen sama, tashoshin teku da sauransu. Aikin da aka kammala na gina tashar teku mai zurfi na Lekki a jihar Legas da ke Nijeriya da ya kai kimanin Dala Biliyan 1.5, daya ne daga cikin ire-irensa masu dimbin yawa a Afirka. Don haka samun ci gaban tattalin arzikin Sin da kashi 5% zai ba ta dama ta samar da karin ayyukan ci gaba a Afirka.

Idan aka fadada zuwa duniya kuwa, ci gaban da kasar Sin za ta samu da kashi 5% zai taimaka wajen cike gibin da ake da shi a duniya, domin cinikayyar fitar da kaya da shigar da su a tsakanin Sin da kasashe za ta habaka. Kana ana sa rai Sin ta ba da gudunmawa ga bunkasar ci gaban duniya a 2023 da kashi 30 cikin 100.

Wannan tsari baro-baro a fili yake cewa babu tantama hakar kasar ta Sin za ta cimma ruwa bisa fafutikar da take yi wajen gina kasa ta zamani mai bin tsarin gurguzu a dukkan sassan rayuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ighalo Yana Son Osimhen Ya Koma Manchester United

Next Post

Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

14 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

15 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

16 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

17 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

18 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

2 days ago
Next Post
Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.