ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Burin Kasar Sin Na Samun Bunkasar GDP Da Kashi 5% A Bana Zai Cika

by yahuzajere
3 years ago
Kasar Sin

Masu zantukan hikima kan ce “da icce mai kama ake kota”, tabbas haka ne, domin duk lokacin da wata kasa ta tasa wani buri a gaba, a kan duba a ga ko abin nan da take son cimmawa mai yiwuwa ne ko zai zama tamkar gurguwa da auren nesa bisa la’akari da matakai da ta dauka da kuma waiwayen abubuwan da ta gudanar a baya.

A bana, kasar Sin ta kudiri aniyar bunkasa tattalin arzikinta da a kalla kashi 5% (cikin dari), kamar yadda firmanistan kasar, Li Keqiang ya sanar a cikin rahoton ayyukan gwamnati da ya gabatar a taron wakilan majalisar jama’ar kasar, ranar 5 ga watan Maris din nan, baya ga kuma za ta samar da sabbin ayyukan yi miliyan 12, daidaita zaman kashe wando a birane da kashi 5.5, karin kashi 3% a mizanin farashin masu amfani da kayan masarufi.

Wannan kudiri da kasar Sin ta tsara cimmawa mai yiwuwa ne saboda dama kasar ba ta kwanta sai da zakara. Da farko abin da za a yi la’akari da shi, shi ne yadda kasar ta rika samun matsakaicin bunkasar tattalin arziki da mizanin 5.2% a cikin shekaru 5 da suka wuce, da kuma iya cin jarrabawar da bullar cutar COVID-19 ta yi mata, sai kuma wasu matakai da a halin yanzu ta dauka don cimma burin nata na samun ci gaba da kashi 5%.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa a shekarar 2022, kasar ba ta iya cimma kason da ta yi hankoron cimmawa a farko-farkon 2022 ba saboda wasu dalilan da suka shafi annobar COVID-19 da koma-bayan tattalin arzikin duniya, amma ta yi kokari da ta samu ci gaba da kashi 3% domin ba abu ne mai sauki a iya samun hakan ba a yanayi mai wuyar sha’ani da kan fado waka’an (ba-zata).

Har ila yau, matakan da kasar ta dauka domin tayar da komada daga COVID-19 a karshen bara da yadda kasar ta nuna kwazo a hada-hadar sarrafa kaya da cinikinsu da kuma ci gaban da ta samu na GDP a sulusin karshe na 2022 da kashi 2.9, duk sun zarce hasashen da aka yi na samun bunkasa, don haka wannan manuniya ce ga yiwuwar cimma burin kasar na bunkasa GDP da kashi 5%.

LABARAI MASU NASABA

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Bugu da kari, tun a farkon wannan shekarar, tattalin arzikin Sin ya samu ci gaba sakamakon kyawawan tsare-tsare da manufofi da gwamnatin kasa da ta kananan hukumomi suka dauka ta bangaren kudi, zuba jari, inganta yanayin kasuwanci da amfani da kayan masarufi da sauransu.

Bayanan da Hukumar Kididdiga ta Sin ta fitar a ranar 1 ga Maris, sun nuna an samu ci gaban sayen kayan da kasar Sin ta sarrafa a watan Fabrairu fiye da na watan Janairu da kashi 2.5. Wannan ya kara gaskata bayanan da aka fitar kwanan baya game da yadda farfadowar tattalin arzikin Sin ke samun ci gaba.

Don haka ma, galibin cibiyoyin da ke auna bunkasar tattalin arziki na duniya sun yi yakini game da habakar tattalin arzikin kasar Sin a bana, inda suka rika daga ma’aunin mizanin da suke hasashe a kai a kai. Misali, Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF), ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Sin zai bunkasa zuwa kashi 5.2% a bana. Haka nan mizanin Cibiyar Nomura Securities ya kyautata hasashen ci gaban zuwa kashi 5.3% daga kashi 4.8%. Ita ma Cibiyar Goldman Sachs ta yi hasashen abin zai kai 5.5%, sai kuma Morgan Stanley da hasashenta ya dara na kowa a cikinsu da ta ce tattalin arzikin na Sin zai bunkasa ne da kashi 5.7%.

Sakamakon dunkulewar tattalin arzikin duniya, ba shakka, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin zai taimakawa ci gaban duniya.

Misali a Afirka, kasar Sin ta zama gagarabadau wajen bunkasa manyan ayyukan more rayuwa a kasashe daban-daban da suka hada da hanyoyi, sufurin jiragen kasa, madatsun ruwa, filayen jiragen sama, tashoshin teku da sauransu. Aikin da aka kammala na gina tashar teku mai zurfi na Lekki a jihar Legas da ke Nijeriya da ya kai kimanin Dala Biliyan 1.5, daya ne daga cikin ire-irensa masu dimbin yawa a Afirka. Don haka samun ci gaban tattalin arzikin Sin da kashi 5% zai ba ta dama ta samar da karin ayyukan ci gaba a Afirka.

Idan aka fadada zuwa duniya kuwa, ci gaban da kasar Sin za ta samu da kashi 5% zai taimaka wajen cike gibin da ake da shi a duniya, domin cinikayyar fitar da kaya da shigar da su a tsakanin Sin da kasashe za ta habaka. Kana ana sa rai Sin ta ba da gudunmawa ga bunkasar ci gaban duniya a 2023 da kashi 30 cikin 100.

Wannan tsari baro-baro a fili yake cewa babu tantama hakar kasar ta Sin za ta cimma ruwa bisa fafutikar da take yi wajen gina kasa ta zamani mai bin tsarin gurguzu a dukkan sassan rayuwa.

Kasar Sin
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
Daga Birnin Sin

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Next Post
Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

Zaben Shugaban Kasa: Kotu Ta Amince Da Bukatar INEC Na Sake Inganta BVAS

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.