• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsokaci A Kan Mazajen Da Ke Bayyana Sirrukan Gidanjensu A Majalisa

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tsokaci A Kan Mazajen Da Ke Bayyana Sirrukan Gidanjensu A Majalisa

Fadila Lamido

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barkanku da kasancewa tare da shafin Taskira, shafin da ke zaqulo muku batutuwa waxanda suka shafi al’umma ta fanni daban-daban, inda a yau shafin namu zai yi duba ne game da irin halin wasu mazan, musamman masu zaman majalisa ta yadda suke bayyana sirrin gidajensu, kamar wajen yin cefane da sauransu.

Wasu mazan yayin da suka bayyana a majalisa ba su da aiki face bayyanawa sauran abokai sirrikansu, kamar misali; “Maggin dana siya tare da kai tuni nawa ya qare”, wani kuma ya ce shi gidansa da mai gwangwani xaya ake girki, wani kuwa zai ce yadda azumi ya kama kudin cefanen gidansa naira dari biyu ne babu qari ta ishi gidansa cefane.

  • A Karon Farko Iyayena Ba Su Amince Da Shigata Fim Ba —Fatima Moh’d
  • Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

Wanda alhalin dukkaninsu da suke tare a wajen ba yawan iyalansu da samunsu daya ba, balle su kwatanta shi ya zamo xaya. Ko mene ne amfanin hakan, kuma me hakan zai iya haifarwa? Dalilin hakan shafin Taskira ya ji ta bakin wasu daga cikin mabiyansa inda suka bayyana nasu ra’ayoyin kamar haka:

Sunana Mas’ud Saleh Dokadawa:

Majalisa
Mas’ud Saleh Dokawa

Wannan dabi’a ce mara kyau wacce bai kamata mutane su rinka yinta ba, Musamman mazaje, magidanta, kididdiga akan abin amfanin yau da kullum kamar cefane da sauransu, bai kamata ba har ma abokai su rinka zuga abokanansu akan yadda za su saka ido ga matayensu, wannan ba daidai bane. Ba shida wani amfani, kuma zai haifar da matsaloli kamar yawan rigima tsakanin mata da miji, rashin yadda, mammako da rashin yalwatawa iyali da kuma rashin fahimtar juna tsakaninsu. Shawara ita ce su ji tsoron Allah su daina, sannan kuma su kiyaye hakkokin iyalensu, su sani cewa hakki ne su kyautatawa iyalansu ba wai takurawa ba, don ba musulunci bane yin hakan, sannan malamai su rinka yawaita huduba da nasihohi akan yalwatawa da farantawa iyali, sannan su sani cewa Allah zai tambaye su akan duk nauyin da aka dora musu na iyalensu, sannan su sani cewa ibada ne in suka yi hakan akwai lada babba don ibada ne.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Sunana Abdulrrashid Haruna daga Jihar Kano:

Majalisa
Abdulrashid Haruna

Na’am a zahiri wannan rashin sanin kimar kai ne, da rashin sanin darajar kai,da rashin sirri, da shegen surutu mara amfani wanda a karshe hakan zai zama cin mutunci ga duk mai fadar sirrin iyalinsa. Hakan bai da wata fa’Ida sai dai ma ila da yake da shi, domin duk wanda ya ke ma labe wata ran zai shigo. Shawara shi ne su fahimci rayuwa kan cewa dan guntun gatarinka ya fi sari ka bani, ni da kai akwai bambanci, haka za abincin mu ma ya bambanta, rayuwa sirri ce kuma ciki ba dan tuwo da ruwa aka yi shi ba, Allah ya kyauta.

Sunana Abubakar Muhammad Shehu daga Jihar Kano:

Majalisa
Abubakar Muhammadu Shehu

Gaskiya yawancin mutane haka suke kuma haka ba daidai bane, amma wasu sun maida shi dabi’a. Gaskiya hakan ba shi da wani amfani wanan yana haifar da rabuwar kan iyali, shawarata a nan haka ba daidai bane kuskure ne babba a kiyaye.

Sunana Fadila Lamido daga Jihar Kaduna:

Majalisa
Fadila Lamido

Bai dace ba, domin wata kila ba yawan dawainiyar ku daya ba, wani daga cikinshi sai na matarshi. Wani kuma akwai yara, idan babu yara tana iya yiyuwa gidanka ana yawan baki. Kuma adadin man da za a zuba a cikin abinci ya danganta ne da yawan abincin, sannan kowacce mace da yanayin salonta wajen sarrafa abinci, kamar misali wasu matan har yanzu suna amfani da gishiri, wasu kuma da maggi kawai suke amfani, wadda bata amfani da gishiri maginta zai riga karewa, idan ma yawanku daya kenan, a takaice dai babu tsari ka zauna kana irin wannan maganar, saka ido ne kawai irin na wasu mazan, wanda zai iya haifar masu da matsala, dan wani  ma ba gaskiya ya fada ba, kawai dai ya kuranta matarshi ne, dan haka rashin wayau ne ka zauna kana nuna matarka na maka barna, zai zama kamar ka nuna gazawarta ne ga abokan ka. Shawarta ga masu aikata irin wannan shi ne; su bari domin hakan kamar suna kushe matan nasu ne a wurin abokai, kuma hakan zai sa abokan suwa matar kallon mabarnaciya, idan ma sun bar zancen a tsakanin su kenan.

Sunana Habiba Mustapha Abdullahi (Dr.haibat) daga Jihar Kano:

Majalisa
Habiba Mustapha Abdullahi

Gaskiya iri-irin waannan abun ya kan jawo tashi hankali da zargi dama rashin zaman lafiya tsakani miji da mata, ya kamata maza su san mai za su rinka yin hira a kanshi saboda zaman majalisa ba waje bude sirrin nayi, ba ko me ake fadawa aboki ba ko dan gudu matsala kuma inka kula da matar ka kai ma za ka ji dadi, ka ga matar ka tayi kyau kuna cikin kwanciyar hankali dan Allah ‘yan uwa da abokai, da iyaye mu duk mai yin haka yayi kokarin gyarawa ko dan gobe yaranmu, azumi wata ne me dinbun samun lada, a gaskiya ba wani amfani illa ya jawo maka magan-ganu marasa dadi saboda ita mace ‘yar a kula ce ko da yaushe tana bukatar kulawar mijinta, kalmomi masu dadi, Allah ya sa mu gyara.

Sunana Osman Abdullahi Mustapha (Abba Goma) daga Jihar Kano:

Majalisa
Usman Abdullahi Mustapha

Shawarata anan majalisa fa ba wajen fadin sirri ko wani matsala da kai tsakaninka da matar ka ba gaskiya ‘yan uwa na maza a gaskiya bai kamata ace muke yi wa mata haka ba, ko ba komai in aka dafa kaima za ka ci, yaranka ma haka, hakan ba shi da wani amfani sai ma kawo rashin zaman lafiya wanda zai haifar da da mara ido, kana da kanwa  da anti da yaya kila ma a gidanku kai ne namiji, haka kuma ba za ka so ace an yi wa daya daga cikinsu haka, dan Allah muyi kokarin magance matsala.

Sunana Yakubu Obida daga Jihar Kano, Farawa, Karamar Hukumar Ungogo:

Majalisa
Yakubu Obida

Gaskiya abin da ya ke faruwa kuskure ne ga maza har mata ma, dan ba maza ne kadai suke irin wannan abun ba, zai yi wahala ka ga namiji ya fita yana bayyana abun da yake faruwa a gidansa. Gaskiya namijin da ya ke irin wannan abun ba daidai bane tsakani da Allah, ka fito waje kana fadar sirrin gidanka, ko amininka ne gaskiya ba kowanne abu bane za ka fito waje kana fada na sirrin gidanka kuskure ne. Hakan ba shida wani amfani, idan har ka dauka ka kai waje, shi wanda ka je ka fadawa za ka ga sai dai ya dawo yana yi maka gori, ko yana yi wa matan gori, ta kowanne bangare akwai matsala, ta ‘ya mace ne ko da namiji, zubar da kima ne da zubar da darajar aure. Duk wani abu da yake tafiya ba daidai ba idan da san samu ne kamata yayi macen taiwa mijin magana, ko shi ya yi wa macen magana, in abun ya gagara ne sai a kai kara zuwa gidansu mijin, ko kuma shi ya kai kara gidansu macen, ina tunnin wannan ita ce mafita. Amma ka dauki zance ka kai waje bai dace ba zai kawo matsaloli da dama kamar zubar da kima a idon wanda aka je aka fadawa, lokacin da ka sanar da mutum daya shi baka san mutane nawa zai je ya sanarwa ba. Idan kuwa magana ne na iyaye mahaifi da mahaifiya sun san yadda za su yi musu a magance matsalar. Shawarar da zan bawa masu irin wannan halin su daina, dan ba dabi’a ce me kyau ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: majalisaMazajeTsokaci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya, Ya Rasu

Next Post

Darussan Da ‘Yan Siyasa Za Su Koya A Zaben 2023

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

4 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

5 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

13 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

17 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

18 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

20 hours ago
Next Post
Darussan Da ‘Yan Siyasa Za Su Koya A Zaben 2023

Darussan Da ‘Yan Siyasa Za Su Koya A Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.