ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

by Abubakar Abba
3 years ago
Shinkafa

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Bincike ya nuna cewa, duk da tsadar kayan aikin noman rani a bana, da manoman shinkfa da na alkama ke fuskanata a jihar Taraba, sun nuna cewa za su samu amfani mai yawa a bana.

Manoman a fadin jihar, sun bayyana cewa, suna sa ran samun amfani mai yawa na wadannan amfanin nan da mako mai zuwa.

  • Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun
  • Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana

Za a fara diban amfanin gonar biyu ne nan da mako biyu a kananan hukumomi Karim-Lamido da Gassol da Lau da Donga, inda za a yankin Shika, fiye da manoma 200 da suka shuka shinkafa sun fara yankanta.

Rahotannin sun nuna cewa, kashi 60 daga cikin dari na gonakin da aka shuka wadannan amfanin biyu, sun kai munzalin fara dibansu, inda moman na ke da yakinin samun amfani mai dimbin yawa, duk da cewa, sun samu kalubalen dizil da man fetur da suke zuba wa a cikin ijinan ban- ruwansu.

Daya daga cikin manoman ranin mai suna Injiya Yahaya Mafindi, ya bayyana cewa, gonarsa ta shinkfa ta fada cikin ambaliyar ruwan a shekarar da ta wuce, saboda haka ta lalatace, hakan ya sa ya fara yin noman rani da wuri a bana, inda ya ce, nan da mako uku yake sa ran yanke shinkafarsa.

Kashi 60 daga cikin dari na gonakin da aka shuka wadannan amfanin biyu, sun kai munzalin a fara dibansu, inda manoman, ke da yakinin samun amfani mai yawa, duk da cewa, sun samu kalubalen dizil da man fetur da muke zuba wa a cikin ijinan ban-ruwa.

Mafindi ya ci gaba da cewa, da farko ya samu rashin kwarin gwiwa da zai fara yin noman na rani, saboda tsadar man fetur da zai zuba a cikin injin ban-ruwa da zai yi amfani da shi a gonarsa.

A cewarsa, yana da injinan ban-ruwa guda uku da yake yin amfani da su don yin ban-ruwa a gonarsa, amma saboda tsadar man fetur, hakan ya sa ya sayo injinan ban-ruwa mai aiki da hasken rana, inda ya shawarci manoman kar su fara tunin yin noman rani a bana idan sun san ba su da isasun kudin da za su sayi man fetur da iri da magungunna feshi da sauransu.

Shi ma wani manoman na rani mai suna Yakubu Dauda, ya bayyana cewa, kashi 50 daga cikin dari na noman rani da ya yi, ya karbo rancen naira 500, 000 a bana, inda ya kara da cewa, yana sa ran samun shinkafar mai yawa.

Sannan kuma, ya nuna jin dadinsa kan rashin kwarin da ke lalata shinkafar da aka shuka sabanin yadda ta auku a shekarar da ta wuce, musamman a karamar hukumar Lau da Karim-Lamido da Gassol, inda ya kara da cewa, kalubalen da manoman suka fuskanta a wannan shekarar shi ne kawai na tsadar man dizill da na man feutur da suke zuba wa injinan ban-ruwa.

Wani manomin shi ma mai suna Alhaji Isa Tafida, wanda yake bai wa manoman rani rancen kudin yin noman na rani a lokacin aikin shinkafa, ya bayyana cewa, yana bayar da rancen ne kashi 50 a cikin dari, musamman ga manoman da suka yi asara saboda ambaliyar ruwan da ta auku a shekarar da ta wuce a yankin, don su sake farafado wa.

Ya kuma ci gaba da cewa, da alaumun manoman na rani a yankin, bana za su samu amfani mai dimbin yawa, inda ya nuna jin dadinsa kan yadda mnoman za su sake fafrfado wa biyo bayan aukuwar ambaliyar ruwan.

“Na bayar da rancen ne kashi 50 daga cikin dari, musamman ga manoman da suka yi asara saboda ambaliyar ruwan da ta auku a shekarar da ta wuce a yankin, musamman don su sake farafadowa.”

A yankunan Tau da kuma Didango da ke a kananan hukumomin Ardo-Kola da Karim-Lamido akasarin manoman na shinkafar da alkamar da aka tattauan da su sun bayyana cewa, suna sa ran  samun amfani mai dimbin yawa.

Daya daga cikinsu, mai suna, Musa Didango ya bayyana cewa, koda yake sun samu kalubalen tsadar kayan aikin na yin noman rani, amma mun ji dadi sosai saboda wa su kalubalen da suka samu na kwarin da ke lalata amfanin gona da kuma na makiyayan da ke tura dabbobinsu cikin gonakinsu.

“Mun ji dadi sosai saboda ba mu fuskanci kalubalen kwarin da ke lalata amfanin gona ba da kuma na makiyayan da ke tura dabbobinsu cikin gonakinmu ba.”

Shinkafa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya, Ya Rasu

Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.