ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

by Abubakar Abba
3 years ago
Shinkafa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Bincike ya nuna cewa, duk da tsadar kayan aikin noman rani a bana, da manoman shinkfa da na alkama ke fuskanata a jihar Taraba, sun nuna cewa za su samu amfani mai yawa a bana.

Manoman a fadin jihar, sun bayyana cewa, suna sa ran samun amfani mai yawa na wadannan amfanin nan da mako mai zuwa.

  • Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun
  • Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana

Za a fara diban amfanin gonar biyu ne nan da mako biyu a kananan hukumomi Karim-Lamido da Gassol da Lau da Donga, inda za a yankin Shika, fiye da manoma 200 da suka shuka shinkafa sun fara yankanta.

Rahotannin sun nuna cewa, kashi 60 daga cikin dari na gonakin da aka shuka wadannan amfanin biyu, sun kai munzalin fara dibansu, inda moman na ke da yakinin samun amfani mai dimbin yawa, duk da cewa, sun samu kalubalen dizil da man fetur da suke zuba wa a cikin ijinan ban- ruwansu.

Daya daga cikin manoman ranin mai suna Injiya Yahaya Mafindi, ya bayyana cewa, gonarsa ta shinkfa ta fada cikin ambaliyar ruwan a shekarar da ta wuce, saboda haka ta lalatace, hakan ya sa ya fara yin noman rani da wuri a bana, inda ya ce, nan da mako uku yake sa ran yanke shinkafarsa.

Kashi 60 daga cikin dari na gonakin da aka shuka wadannan amfanin biyu, sun kai munzalin a fara dibansu, inda manoman, ke da yakinin samun amfani mai yawa, duk da cewa, sun samu kalubalen dizil da man fetur da muke zuba wa a cikin ijinan ban-ruwa.

Mafindi ya ci gaba da cewa, da farko ya samu rashin kwarin gwiwa da zai fara yin noman na rani, saboda tsadar man fetur da zai zuba a cikin injin ban-ruwa da zai yi amfani da shi a gonarsa.

A cewarsa, yana da injinan ban-ruwa guda uku da yake yin amfani da su don yin ban-ruwa a gonarsa, amma saboda tsadar man fetur, hakan ya sa ya sayo injinan ban-ruwa mai aiki da hasken rana, inda ya shawarci manoman kar su fara tunin yin noman rani a bana idan sun san ba su da isasun kudin da za su sayi man fetur da iri da magungunna feshi da sauransu.

Shi ma wani manoman na rani mai suna Yakubu Dauda, ya bayyana cewa, kashi 50 daga cikin dari na noman rani da ya yi, ya karbo rancen naira 500, 000 a bana, inda ya kara da cewa, yana sa ran samun shinkafar mai yawa.

Sannan kuma, ya nuna jin dadinsa kan rashin kwarin da ke lalata shinkafar da aka shuka sabanin yadda ta auku a shekarar da ta wuce, musamman a karamar hukumar Lau da Karim-Lamido da Gassol, inda ya kara da cewa, kalubalen da manoman suka fuskanta a wannan shekarar shi ne kawai na tsadar man dizill da na man feutur da suke zuba wa injinan ban-ruwa.

Wani manomin shi ma mai suna Alhaji Isa Tafida, wanda yake bai wa manoman rani rancen kudin yin noman na rani a lokacin aikin shinkafa, ya bayyana cewa, yana bayar da rancen ne kashi 50 a cikin dari, musamman ga manoman da suka yi asara saboda ambaliyar ruwan da ta auku a shekarar da ta wuce a yankin, don su sake farafado wa.

Ya kuma ci gaba da cewa, da alaumun manoman na rani a yankin, bana za su samu amfani mai dimbin yawa, inda ya nuna jin dadinsa kan yadda mnoman za su sake fafrfado wa biyo bayan aukuwar ambaliyar ruwan.

“Na bayar da rancen ne kashi 50 daga cikin dari, musamman ga manoman da suka yi asara saboda ambaliyar ruwan da ta auku a shekarar da ta wuce a yankin, musamman don su sake farafadowa.”

A yankunan Tau da kuma Didango da ke a kananan hukumomin Ardo-Kola da Karim-Lamido akasarin manoman na shinkafar da alkamar da aka tattauan da su sun bayyana cewa, suna sa ran  samun amfani mai dimbin yawa.

Daya daga cikinsu, mai suna, Musa Didango ya bayyana cewa, koda yake sun samu kalubalen tsadar kayan aikin na yin noman rani, amma mun ji dadi sosai saboda wa su kalubalen da suka samu na kwarin da ke lalata amfanin gona da kuma na makiyayan da ke tura dabbobinsu cikin gonakinsu.

“Mun ji dadi sosai saboda ba mu fuskanci kalubalen kwarin da ke lalata amfanin gona ba da kuma na makiyayan da ke tura dabbobinsu cikin gonakinmu ba.”

Shinkafa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya, Ya Rasu

Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.