• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Samar Da Fasfo Fiye Da Miliyan 1.8 A 2022, Yayin Da Ta Bude Ofishin Fasfo A Daura

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Samar Da Fasfo Fiye Da Miliyan 1.8 A 2022, Yayin Da Ta Bude Ofishin Fasfo A Daura
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bisa kokarinta na kara inganta ayyukan ta, hukumar kula da shige da fice ta kasa NIS, ta bayyana cewa, ta samar da fasfo sama da miliyan 1.8 A 2022, abin da ya ninka wanda ta samar a 2021.

Shugaban hukumar na kasa, CGI Isah Jere Idris MFR ya bayyana hakan a garin Daura da ke a cikin jihar Katsina a lokacin bude ofishin fasfo a garin na Daura ranar Laraba.
Jere ya bayyana cewa, bude ofishin Fasfo na Daura, ya kara tabbatar da kokarin mahukuntan hukumar na saita hukumar don ta kai mataki irin na duniya wajen gudanar da ayyukanta.

  • Kaddamar Da Ofishin NIS Na Ilesa Zai Kara Habaka Aikin Fasfo Ga ‘Yan Nijeriya – Isah Jere

Jere wanda ya sanar da hakan a cikin jawabinsa ya ce, ba tare da wata tantama ba, kaddamar da ofishin da kuma sauran makamancinsa da hukumar ta aiwatar, ya nuna a zahiri irin kokarin hukumar na sauke nauyin da aka dora mata na samar da fasfo ta internet don ya kai ga daukacin al’ummar kasar nan.

Shugaban ya ci gaba da cewa, bayar da fasfo din ta hanyar internet ga hakikanin ‘yan Nijeriya, na daya daga cikin nauyin da ke a kan hukumar wanda sashi na biyu na dokar hukumar ta shekara 2015 da aka sabunta ya dora mata.

A cewarsa, shekaru da dama da suka gabata, an samu gagarumin ci gaba wajen sauye -sauyen samar da fasfo daga tsohon tsari zuwa na zamani, inda ya ce, a yanzu an sabunta tsarin zuwa na internet.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

Jere ya yi nuni da cewa, a yanzu ana kara samun bukatar fasfo a kasar nan, inda ya ce, a saboda hakan ne, hukumar hukumar ta kara mayar da hankali don ta cimma wannan kalubalen.

Ya ci gaba da cewa, a shekarar da ta wuce kawai, hukumar ta samar da fasfo miliyan 1.8, wanda ya rubanya wanda ta bayar har sau biyu a 2021.

Shugaban ya ci gaba da cewa, ana kuma ci gaba da yin kokari, don a bude wasu ofisoshi na fasfo a daukacin fadin Nijeriya don a rage cunkoson da ake samu na samar da fasfo a kasar nan, inda ya ce, a ranar Litinin an kaddamar da ofishin samar da fasfo a Ilesha.

Ya bayyana cewa, na garin Daura da aka kaddamar, ya bi sahun na Alimosho da ke a cikin jihar Lagos, inda ya sanar da cewa, na garin Zariya da ke a cikin jihar Kaduna da na Ilesha da ke a jihar Ogun, an bude su a wajen manyan birane ne na jihohinsu.

Ya ci gaba da cewa, don a tabbatar da an tantance bayanan masu buqatar fasfo, an hada bayanan na su da shedar katin dan kasa ta NIN.

Ya ce, inganta samar da fasfo ta internet ya zo ta fannoni da dama wanda ya hada da, na tsawon shekara goma, inda ya ce, bisa ga wannan takardun, masu buqatar fasfo a yanzu za su iya yin amfani da tsarin da suke bukata na mallakar fasfo ta internet.

A cewarsa, Nijeriya ce ta farko a Nahiyar Afrika da ta juya zuwa ga irin wannan tsarin na samar da fasfo ta internet, inda ya shawarci masu bukatar fasfo da su juya zuwa ga irin wannan tsarin na neman fasfo don bukata da kuma biyan kudin su ta shafin internet na hukumar: .immigration.gov.ng) da suke bukata.

Ya yaba wa gwamnatin tarayya kan amincawa da aikin na samar da fasfo ta internet wanda ya ke daga cikin yin amfani da fasahar zamani a iyakokin kasar nan, inda ya ce, bisa goyon bayan ‘yan hadaka an samun damar yin aiki akan lokaci na samun bayanan masu shigowa cikin kasar nan.

Ya kara da yin godiya ce, a madadin ma’aikatan hukumar, yana mai cewa, “musamman muna gode wa ministan kula da harkokin cikin gida Rauf Aregbesola, bisa goyon bayan da ya ke ci gaba da ba mu da kuma irin gudunmawar da sauran masu ruwa da tsaki har da gudunmawar da gwamnatocin jihohi da sarakunan gargajiya ke bamu.”

CGI Jere ya ba da tabbacin hukumar ta NIS za ta ci gaba da bunkasa dukkan ayyukan da tsarin mulkin kasa ya dora mata bilhakki tare da kyautata mu’amala da abokan hulda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DauraFasfoHukumaJereNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Da Yawunmu Gawuna Ya Taya Abba Gida-gida Murna Ba – APC Kano 

Next Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kashe Naira Biliyan 24.2 Don Samar Da Intanet Kyauta

Related

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
Labarai

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

2 hours ago
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
Manyan Labarai

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

4 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara

6 hours ago
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano
Manyan Labarai

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

7 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

15 hours ago
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
Labarai

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

17 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Za Ta Kashe Naira Biliyan 24.2 Don Samar Da Intanet Kyauta

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kashe Naira Biliyan 24.2 Don Samar Da Intanet Kyauta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.