• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Kasa Barci A Daren Da Zan Fara Fitowa Fim Karon Farko —Mudassir Isyaku

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
in Nishadi
0
Na Kasa Barci A Daren Da Zan Fara Fitowa Fim Karon Farko —Mudassir Isyaku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shafin da ke zakulo muku fitattun Jarumai da mawaka manya da knana dake cikin masana’antar shirya fina-finan hausa ta Kannywood, har ma da wadanda suka yi fuce, Shafin yau na tafe da daya daga cikin masu shirya fina-finan Hausa kuma Jarumi me taka rawa a cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood wato MUDASSIR ISYAKU D.T.M, Jarumin da ke taka rawa cikin fina-finan da ke haskawa a yanzu, Jarumin ya bayyana babban kalubalen daya fuskanta bayan shigarsa cikin masana’antar Kannywood, baya ga haka Jarumin yayi karin haske ga masu kallo da masoyansu, dangane da irin rashin lokutan da sauran Jarumai ke rasawa yayin da suke bukatarsu, tare da kira ga gwamnati wajen magance matsalolin da ke afkuwa a cikin masana’antar, har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai tattaunawar tare da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA Kamar haka:

Masu kartu za su so su ji cakakken sunanka.
Sunana Mudassir Isyaku D.T.M ma’anar D.T.M ‘Dutsan-ma Katsinma state channel’ garin iyayena, amma ni an haife ni a Jihar Kano Rijiyar Lemo.

Ko za ka fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?
Tarihina shi ne; Na yi ‘Primary school’ a Rijiyar lemo ‘Sulaiman Chamber’, nayi ‘Secondary School, Warure Gwale Local Gobernment’, a yanzun haka ana ci gaba da yi. Ba ni da aure, aure sai nan gaba in na samu wadda take sona.

Wanne mataki ka tsaya a karatunka, kuma bayan karatu kana aiki ne ko iya karatun kake yi?
Ina matakin N.C.E, kuma ina aiki, ni Furodusa ne kuma Jarumi a masa’antar Kannywood.

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?
Tun ina karami nake son harkar fim, don bana mantawa a kafa nake zuwa Mandawari Sabon Titi ofis din ‘DIRECTOR ISHAK SIDI ISHAK’ ba don komai ba sai don in ga ‘yan fim.

Labarai Masu Nasaba

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

Mudassir Isyaku

Za ka yi kamar shekara nawa cikin masana’antar Kannywood?
Zan kai shekara 6, da fara ‘acting’ kuma shekara 2.

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?
An sha wuya shiyasa yanzun Alhamdulillah, don daga gida za ka fara fuskantar kalubale.

Wanne irin kalubale ka fuskanta daga wajen iyayenka lokacin da ka fara sanar musu kana son shiga cikin masana’antar?

Wurin mahaifina na samu dama, wurin ‘yan uwa kuma dangin mahaifina sune suka runka bani matsala tun daga Katsina aka zo aka gayawa mahaifina an ganni a fim, amsar daya bayar ita ta bani dama, sakamakon ni yadda nake tunani ba zai bar ni in yi fim ba, don haka ni ban gaya masa ba kuma zan je ‘location’, amma ba zan fito a inda za a ganni ba, sai wurin taron jama’a. Sai muka je wani fim BABAN SADIK na Nafisa da Adamu na fito a kotu.

Ya farkon fara shirya fina-finanka ya kasance, musamman yadda za ka ji wasu na kukan samun faduwa a farkon farawarsu, shin kai ya abin ya kasance ko kwalliya ta biya kudin sabulu?
Haka ne, amma gaskiya ni na san komai, in baki manta ba na gaya miki cewa na dade, kawai dai ni ba zan yi ba, har sai da amincewar mahaifina, kuma dama shi fim mataki ne akwai nasarori da dama a ciki.

Wanne fim ka fara shiryawa, kuma za su kai kamar guda nawa?
BANI DA LAIFI da WATA RANA, kusan a tare na yi su, za su kai kamar guda biyar.

A wanne fim ka fara fitowa, kuma wacce rawa ka taka cikin fim din?
Fim djn dana fara fitowa WATA RANA.

Ya ka ji a lokacin da za ka fara fitowa a fim matsayin jarumi ba mashiryin shirin fim ba?
Ana gobe za a fara ‘Shooting’ kasa bacci na yi, saboda murna, wurin gabatar da fim din kuma aka hada ni da TAHEER FAGGE da LADIDI FAGGE sai suka bani kwarin gwiwa.

Bayan shigarka masana’abtar Kannywood ko akwai wani kalubale da ka ci karo da shi cikin masana’antar?

Mudassir Isyaku
Kwarai kuwa, kalubalen dana fuskanta wanda ba zan taba mantawa da shi ba a cikin masana’antar Kannywood shi ne; Akwai wata rana da wani bawan Allah ya kira ni, ya ke ce mun ya tsinci wata waya na zo na karba, kuma aka ci sa’a a unguwarmu ne a tsallake, da na ne sai na na yi mamaki wai ya ga lambata a ciki. haka na yi ta bin shi na ce “kai! ni ban san wannan number ba”, a karshe dau na gano wani ma’aikacin ‘Police’ a ‘wani dibision anan unguwarmu. Kin san yanayin fim idan kana yi za ka gane wani abun, Na gano shi sa’in daya fara magana, yanayin yadda ya ke magana ko ’emotion” dinsa za ka yi ‘understanding’. Sai na ce masa “ka ga bawan Allah a ina kake?”, ya ce shi dan sanda ne, a ina? ya fadan sai na ce masa ‘me ya ke faruwa yi mun bayani?”, shi ne ya ke bani labarin zargin da ke tsaninsa da matarsa, Ta fita ta tafi ba a san inda ta tafi ba, duk garinsu Katsina gidan iyayenta da ko ina amma ba a ganta ba, duk gidan ‘Yan uwanta na Kano da Katsina ba a ganta ba, sai da tayi kwana goma, sannan ta dawo. Tana dawowa sai ya kwace wayarta, yana karbar wayar sai yayi ‘Searching’ din lamba sai ya ga lambata kuma an rubuta ‘My’. Toh! sai ya ce mun wayar ta mace ce, sai na ce wace ce ita macen?, sai ya ce ‘wannan macen ai da alamun sunanta Nafisa”, anan na fada masa ina da Nafisa kuma a Katsina take, amma ita uwa ce a wurina, ya ce “eh! ita ma a Katsina take”, na ce a wanne gari? ni a Dutsanma take, ya ce shi kuma a Batagarawa, kin ga mun dan samu kilashin. Sai ya ce mun “A gaskiya….!” na ce “ka ga bawan Allah, wannan dogon turancin da muke fito gaya mun, me ya ke faruwa?”, sai ya ce gaskiya matarsa ce, ya labartan labarin yadda aka yi, ya ce bayan ta dawo ya karbi wayarta yana dubawa ya ga lambata ta sa “My”, na ce toh ni nafisar da nake da ita da ta sa My sai da ta karasa My son. A karshe dai sai na gano ashe irin matan nan ne da za su ga ‘number’ a cikin fim su dauka, wannan ‘case’ din abun ya batan rai, kuma ya tayar mun da hankali, dan akwai kanina ‘Police’ na kira shi, kafin ma wannan lokacin shi police din na kira shi na ce kana ina yanzu?, sai ya ce ya akai? na ce yana ina zan je na same shi, ai maganar aure ba abun wasa bane, na ce ni furodusa ne ina shirya fim, kuma zan iya sa number na a cikin fim ta gani ta dauka, da kansa ya ke cewa ba sai na zo ba, karshe dai washegari sai da na kira wannan kanin nawa muka je har gurin nake masa maganar. Sai ya ke cewa ai shi tun daga maganar da ya ji ina cewa yana ina na zo na same shi? ya ji cewa ba hannuna, sabida in ba ni da gaskiya ba zan nemi inda yake ba, tunda ya fada mun shi ‘Police’ ne. Toh wannan kadan daga cikin irin kalubalen dana fuskanta a cikin fim, wanda ko yaushe bana ita mantawa da shi.

Za mu cigaba a mako mai zuwa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in Morocco Ya Yabawa Gudummawar Da Sin Ta Bayar Wajen Inganta Harkokin Kiwon Lafiya A Kasar

Next Post

Sin Tana Son Ba Da Gudummawar Hikima Don Inganta Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankin Gabas Ta Tsakiya

Related

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

3 days ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

1 week ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

2 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

3 weeks ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

1 month ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

1 month ago
Next Post
Sin Tana Son Ba Da Gudummawar Hikima Don Inganta Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankin Gabas Ta Tsakiya

Sin Tana Son Ba Da Gudummawar Hikima Don Inganta Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankin Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.