ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

by Rabi'at Sidi Bala
9 months ago
Wanda

Wannan ci gaban hirar da wakiliyarmu Rabi’at Sidi Bala ta yi da jaruma a masana’antar Kannywood Hauwa Garba wadda aka fi sani da Sabuwa. A yi karatu lafiya

Wane abu ne ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin haka, wanda ba za ki taba mantawa da shi ba, game da fim?

  • Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
  • Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Gaskiya ne, ba zan taba mantawa da jama’ar da Allah ya ba ni ba, kuma a harkar ce. Da ban shiga Kannywood ba kila ba za a sanni ba, amman na shigo Kannywood da taimakon Allah, kuma gashi Allah ya sa kowa ya sanni, ba inda zan shiga ba a ce wance ba. Kuma duk wani abu da za a ci, a sha, a saka a baki, wallahi bai gagare ni ba, Allah ya rufa min asiri. To, ko wannan ma ai abun farinciki ne da jin dadi.

ADVERTISEMENT

 

Ya ki ka dauki fim a wajenki?

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Na dauki fim sana’a, kuma sana’ar ce. Dan wallahi sana’a ce me kyau ma, ta ba ni gida, ta ba ni mota, na ci, na koshi. Yanzu idan zan shekara na ce ba zan fita ba, a cikin gidana ne, kuma darajar Kannywood. Ina finafinai na a haka na samu gidana, na gina gidan kuma nake zaune cikinsa.

 

Ko kina da ubangida, a cikin masana’antar Kannywood?

Ai ni a masana’antar duk wani sa’a na, ko wanda ya girmen ubangidana ne, ni ba butulu ba ce da zan ce ban da iyayen gida.

 

Ana rade-radin akwai yaranki a cikin masana’antar Kannywood, mene ne gaskiyar maganar?

‘Ya ta guda daya ce take Kannywood, saboda da kanta ta ce “Umma ina so na rika irin sana’ar ku” na ce mata to. Na sa ta tambayi babanta, ‘yan’uwana duk aka tattarasu aka yi musu maganar, suka ce ba komai ni ma ai ina yi. Ta ce “Umma fita za ki yi?” na ce, ba zan fita ba kowa ya yi, ai masana’anta ce me hada da da uwa da uba da kaka da jikoki, da tattaba kunne ce. Na ce ta je Allah ya sa albarka, a lamarin kuma na barta tana yi. Sunanta Maryam Intike.

 

Bayan sana’ar fim, kina wata sana’ar ne?

Eh, ina sana’a. Amma sana’a ta, idan na tashi zan je kudu sarin kaya, ina saro kaya a kudu kamar; Takalma, Sarka da ‘Yan’kunne, irin su Jigida na mata, duk ina saro su. Sannan in zan tafi kuma daga nan, ina tafiya da; Magarya, Kurna, Taura, Tsamiyar Biri, Aduwa, Iloka, Tuwon Madara, Goruba garinta da guda-gudar ta da bararriya mara kwallo. Duk ina kukkulla su ina tafiya da su, da Turaren Humra, Kwalakca, da turaren wuta, ina tafiya da soyayyiyar Fara me rai da lafiya, da Dambun Nama. Duk ina zuwa da su Kudu, idan na gama siyar da su, sai na siyo wadannan kayan sai na dawo. Amma a shekara, sau daya nake zuwa. Sannan ina siyar da Shadda, Atampa, Gyale, amma gaskiya su Katsina nake kai su wajen ‘yar’uwa ta ita take siyar min, sai karshen wata ta turo kudin, sai a kara siya a tura. Nan ma idan mutum na so ya tura min, zan bayar, ina siyar da Huluna irin na maiduguri, amma su kwannan nan na fara.

 

Shin kin taba fuskantar wani kalubale daga wajen masu kallo, musamman wajen fita unguwa ko kasuwa ko makamancin hakan?

Masu kallon nan indai ba farin sani suka yi min ba to, ba za su taba iya gane ni ba. Ni ba a gane ni, in har aka ga an gane ni daman mutum yana mu’amula da ni. Shi ya sa nake shiga cikin kasuwa na yi duk abin da zan yi na dawo ba ruwa na. Ba wanda zai ce ‘Yar’auta, ban taba saka nikab na shiga kasuwa ba, fuskata ‘free’ nake shiga Kasuwa. Ko’ina kuma ina zuwa in har na ga an gane ni to, zan sauri na bar wajen kar a tara min jama’a. Kin san in aka tara maka mutane sai a zo a yi abin da ba daidai ba, ba wai muna gudun jama’a ba, dole ka so jama’a dan su ka ke yi. Amma wani lokacin sai a tara maka jama’a ga wane-ga wane wani can da gudu zai rugo ya zo ya yi maka illa ana tunanin so ne, nan kuma ga wani can baragurbi ya shigo.

 

A misali ki zama shugaba cikin masana’antar Kannywood, wane irin gyara ko cigaba za ki kawo a masana’antar Kannywood?

Idan na zama shugaba a Kannywood me fada a ji, wallahi duk ranar Alhamis da Juma’a in sha Allahu sai na saka malamai ai ta yi mana addu’a, duk abin da yake ba na daidai ba Allah ya fidda mana a cikin Kannywood. Abin da yake na daidai Allah ya kara daukaka shi ya darajanta shi, ya kara mana albarka a cikinsa. Tunda akwai abin da ake baka san da shi ba, kana shugaba ba komai za ka sani ba. Kawai addu’a ita ce gaba, ka zama kai kullum me addu’a ne kamar yadda ka ke a gidanka.

 

Wane sako ki ke da shi ga masoyanki, masu kallon finafinanki?

Abin da zan ce da masoyana, yadda ku ke so na, ku ke kallon finafinau na Allah ya saka muku da alkhairi, kuma ina godiya Allah ya raya muku zuri’a. Sauran yara Allah ya basu ilimi na addinin musulunci.

 

Wacce shawara za ki bawa masu kokarin shiga cikin masana’antar Kannywood?

Shawarar da zan ba su mazansu da matansu, na farko dai su rike salloli, su rika addini cikin lokaci. Sun ga yadda ake farfadar magana a kanmu, dan Allah ku rika addini kuna rokon Allah, Allah zai kubutar da mu da ku akan makiya. Sannan kuma ku zauna lafiya da iyayenku, idan iyayenku na da rai ku yi ta kyautata musu, Allah zai kyautata muku. Sannan ku zama masu ladabi da biyayya a cikin masana’antar, in aka ce ka yi to, ka yi, in aka ce ka bari to, ka bari. Sannan kuma duk wani baragurbi na cikin masana’antar komai girmansa, in mata ne ya neme ku da wata maganar banza, ku je ku kai wa manyan mu za su dauki mataki da iznin Allah.

 

Ko kina da wata shawara da za ki bawa, sauran abokan aikinki dake masana’antar Kannywood?

Kiran da zan yi ga abokan sana’a ta, manyanmu ni dai zan kira, ya kamata a tattara mu bakidaya, a zauna a yi babban ‘meeting’ na kowa da kowa manya da yara. A nuna mana dan’uwan mu idan ya fito ba shi da lafiya, mu ya kamata mu taimake shi, ba a je can a yi ta talla, a je nan ba. Mu tsaya mu hada kai mu taimake shi idan ba shi da lafiya. To, wallahi akwai mutum biyu ban da lafiya ko yanzu watana biyu ban da lafiya, wallahi tallahi akwai wani aiki da muke yi me suna ‘SO NE’ na Sultan. Sai na ga ai yana da kirki ban taba aiki da shi ba sai wannan, ina asibiti ba ni da kudi ga kudi sun kare, ga allurori ba kudi, aka ce a cikin ‘yan fim din mu wa zan kira? na duba lambar mutum biyu na gani, da ta Sultan da ta Daushe. Na kira Daushe na ce “Daushe kai wa girman Allah ka taimaka min, ba ni da lafiya ko wani abu ne ka bayar, gashi kudi sun kare min muna asibiti” ya ce na bari yana mota idan ya sauka zai kira ni. Wannan maganar da nake wata biyu kenan har yau bai kira ni ba. Sultan na kira shi, na fada masa ba ni da llafiya ina asibiti, ya ce Asibiti lafiya? na ce ban da kudi, kudin mu sun kare wajen dubu arba’in mun siyi magunguna da ake yi min karin ruwa da allurai. Sai ya ce min to! nawa ne sauran? ya ce na tambaye su, aka rubuto magnguna wajen likita, aka rubuta magani dubu dari da ashirin da biyar. Da na tashi na kira Sultan na fada masa kudin, ya ce sun yi yawa, na ce, za ka iya bayar da ko ya ya ne, wani ma sai ya bayar a haka har a hada, sai ya ce turon lambar bankinki na tura masa. Aka wuni bai turo ba, aka kwana bai turo ba, akai ta wuni ana kaiwa dare. Sai na ce maman mu bari na kara kiransa, sai ta ce to, sai na kira shi. Ina kiransa ya daga ya ce min a’a Auta, ina zuwa yanzu-yanzun nan da daddaren nan za ki ga abin da zan turo miki. Na ce, to! na gode, Allah ya saka da alkhairi. Kin ga har yau bai kara yi min magana ba to, ta ina za a ce muna taimakon junan mu. A dawo daidai manyan mu a rika taimakawa juna, a daina sa mu a media kowa yana jin maganar mu in dan Allah ne.

Muna godiya, ki huta lafiya.

Wanda
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A 29-05-2027
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.