• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitocin Sin Masu Aikin Jinya A Afirka Sun Zamo Jakadun Wanzar Da Kawance

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Likitocin Sin Masu Aikin Jinya A Afirka Sun Zamo Jakadun Wanzar Da Kawance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A bana ne ake cika shekaru 60 tun bayan da kasar Sin ta fara aikewa da jami’an kiwon lafiya masu aikin jin kai zuwa kasashen Afirka daban daban. A sassa da dama a nahiyar Afirka, tawagogin likitocin na Sin sun yi rawar gani, wajen taimakawa mazauna wuraren, har ta kai ana kiran su da “Wakilai na gari kuma jakadun wanzar da kawance”, matsayin da ko shakka babu ya dace da godiyar da al’ummun nahiyar ke yiwa wadannan jami’ai masu aikin sadaukar da kai.

Tun bayan aikewa da tawagar irin wadannan likitoci na Sin zuwa kasar Aljeriya a watan Afrilun shekarar 1963, Sin ta ci gaba da aikewa da tawagogi daban daban zuwa Afirka. Baya ga kayan aiki da horaswa a fannin sanin makamar aiki da tawagogin ke samarwa a nahiyar.

  • Xi Ya Yi Kira Da A Nace Ga Alakar Sin Da Faransa Bisa Manyan Tsare-Tsare

Cikin sama da shekarun nan 60, Sin ta aike da tawagogin tallafin jinya mai kunshe da jimillar mambobi 30,000 zuwa kasashe da yankunan duniya 76, a sassan nahiyoyin duniya 5. Wasu alkaluman sun nuna cewa, adadin marasa lafiya da rukunonin likitocin Sin masu aikin jin kai suka yiwa jinya ya kai miliyan 290. Kaza lika a yanzu haka, wasu tawagogin likitocin na Sin na aiki a wurare 115 dake kasashe 57, kuma kusan rabin su na aiki ne a wurare masu wuyar kaiwa da yanayi mai tsanani.

Sanin kowa ne cewa nahiyar Afirka na shan fama da cututtuka masu yaduwa, kamar zazzabin cizon sauro ko Malaria, da Amai da gudanawa, da zazzabin shawara da sauran su, cututtukan da masana ke cewa karancin ababen more rayuwa ta fuskar kiwon lafiya, da kwararrun jami’an lafiya ne ke kara ta’azzara yaduwar su. Don haka ne ma rukunonin likitocin da Sin ke turawa suka dukufa, wajen samar da jinya ga dubun dubatar al’ummun nahiyar masu bukatar taimako.

Ko shakka babu rukunonin likitocin Sin sun cancanci yabo, bisa yadda suka gudanar da aikin tiyatar zuciya irin sa na farko a kasar Sudan, da dashen na’urar taimakawa zuciya irin sa na farko a Gambia, da aikin kwakwalwa irin sa na farko a kasar Benin, da dashen kafada a Mozambique da dai sauran su.

Labarai Masu Nasaba

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

Cikin wadannan shekaru 60 da Sin ta shafe tana agazawa nahiyar Afirka ta fuskar kiwon lafiya, al’ummun nahiyar na ta jinjinawa moriyar da suka samu daga wannan aiki. Kuma a wannan gaba da Sin da kasashen Afirka ke kokarin gina al’umma mai makomar bai daya a sabon zamani, ciki har da fannin kula da lafiyar al’umma, tabbas likitocin Sin dake halartar ayyukan tallafawa al’umma a Afirka, na kan gaba wajen taimakawa cin nasarar wannan manufa.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

Next Post

Yadda Tsarin Demokuradiyya Ya Samu Cikakkiyar Daraja A Kasar Sin

Related

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne
Daga Birnin Sin

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

24 minutes ago
Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

1 hour ago
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

19 hours ago
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar
Daga Birnin Sin

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

19 hours ago
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

20 hours ago
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

21 hours ago
Next Post
Kasar Sin

Yadda Tsarin Demokuradiyya Ya Samu Cikakkiyar Daraja A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

September 10, 2025
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

September 10, 2025
Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

September 10, 2025
An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

September 10, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.