ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitocin Sin Masu Aikin Jinya A Afirka Sun Zamo Jakadun Wanzar Da Kawance

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A bana ne ake cika shekaru 60 tun bayan da kasar Sin ta fara aikewa da jami’an kiwon lafiya masu aikin jin kai zuwa kasashen Afirka daban daban. A sassa da dama a nahiyar Afirka, tawagogin likitocin na Sin sun yi rawar gani, wajen taimakawa mazauna wuraren, har ta kai ana kiran su da “Wakilai na gari kuma jakadun wanzar da kawance”, matsayin da ko shakka babu ya dace da godiyar da al’ummun nahiyar ke yiwa wadannan jami’ai masu aikin sadaukar da kai.

Tun bayan aikewa da tawagar irin wadannan likitoci na Sin zuwa kasar Aljeriya a watan Afrilun shekarar 1963, Sin ta ci gaba da aikewa da tawagogi daban daban zuwa Afirka. Baya ga kayan aiki da horaswa a fannin sanin makamar aiki da tawagogin ke samarwa a nahiyar.

  • Xi Ya Yi Kira Da A Nace Ga Alakar Sin Da Faransa Bisa Manyan Tsare-Tsare

Cikin sama da shekarun nan 60, Sin ta aike da tawagogin tallafin jinya mai kunshe da jimillar mambobi 30,000 zuwa kasashe da yankunan duniya 76, a sassan nahiyoyin duniya 5. Wasu alkaluman sun nuna cewa, adadin marasa lafiya da rukunonin likitocin Sin masu aikin jin kai suka yiwa jinya ya kai miliyan 290. Kaza lika a yanzu haka, wasu tawagogin likitocin na Sin na aiki a wurare 115 dake kasashe 57, kuma kusan rabin su na aiki ne a wurare masu wuyar kaiwa da yanayi mai tsanani.

ADVERTISEMENT

Sanin kowa ne cewa nahiyar Afirka na shan fama da cututtuka masu yaduwa, kamar zazzabin cizon sauro ko Malaria, da Amai da gudanawa, da zazzabin shawara da sauran su, cututtukan da masana ke cewa karancin ababen more rayuwa ta fuskar kiwon lafiya, da kwararrun jami’an lafiya ne ke kara ta’azzara yaduwar su. Don haka ne ma rukunonin likitocin da Sin ke turawa suka dukufa, wajen samar da jinya ga dubun dubatar al’ummun nahiyar masu bukatar taimako.

Ko shakka babu rukunonin likitocin Sin sun cancanci yabo, bisa yadda suka gudanar da aikin tiyatar zuciya irin sa na farko a kasar Sudan, da dashen na’urar taimakawa zuciya irin sa na farko a Gambia, da aikin kwakwalwa irin sa na farko a kasar Benin, da dashen kafada a Mozambique da dai sauran su.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Cikin wadannan shekaru 60 da Sin ta shafe tana agazawa nahiyar Afirka ta fuskar kiwon lafiya, al’ummun nahiyar na ta jinjinawa moriyar da suka samu daga wannan aiki. Kuma a wannan gaba da Sin da kasashen Afirka ke kokarin gina al’umma mai makomar bai daya a sabon zamani, ciki har da fannin kula da lafiyar al’umma, tabbas likitocin Sin dake halartar ayyukan tallafawa al’umma a Afirka, na kan gaba wajen taimakawa cin nasarar wannan manufa.(Saminu Alhassan)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Next Post
Kasar Sin

Yadda Tsarin Demokuradiyya Ya Samu Cikakkiyar Daraja A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.