• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisa Ya Bayar Da Tallafi Tare Da Koyar Da Sana’o’i A Zariya

by Idris Umar
2 years ago
in Labarai
0
Dan Majalisa Ya Bayar Da Tallafi Tare Da Koyar Da Sana’o’i A Zariya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daruruwan mutane ne suka amfana da tallafi daga dan majalisa mai wakiltar karamar karamar hukumar Sabon Gari ta jihar Kaduna.

 

Tallafin da dan majalisa ya bayar ya taba bangarori da dama na rayuwar al’umar karamar hukumarsa ta Sabon Gari.

  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

Baya ga tallafin abinci da dan majalisa ya bayar ga darurun jama’a tuni ya shirya taron koyar da sana’ar dogaro da kai ga daruruwan jama’arsa.

 

Labarai Masu Nasaba

ÆŠan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

Wakilinmu ya ziyarci dukkan bangaren da ake bayar da horon don tabbatar wa idonsa abin da ke gudana a wajen. Wajen da ake bayar da horon ga daruruwag al’ummar ta karamar hukumar guda 2 ne kuma duk cike yake da mutane

 

Da yake zantawa da manema labarai, mai taimakawa dan majalisar a bangaren harkar gudanarwa, Kwamred Ishak Adamu (A.D.O) ya bayyana dukkan abubuwan da dan majalisan ya gudanar a ‘yan kwanakin nan wato kafin shigar watan Azumi da cikin watan azumin duk a matsayin tallafi ga jama’arsa karkashin jam’iyarsu ta APC.

 

Ishak Adamu ya ce, “A yanzu haka mutane 700 ake ba horo maza da mata da samari da har da tsofafi dukkansu ana basu horo ne na koyan kananan sana’o’i kamar yadda za su iya hada alkaki na zamani ko yadda za su hada kek na zamani kuma in sun kammala samun horon dan majalisa zai ba su naira dubu ashiri da biyar (#25,000) ga ko wanne da ya sami horon don yin jali.”

 

Mataimakin na musamman ya kara da cewa satin da ya gabata ma dan majalisar ya bayar da buhun shinkafa manya da kanana guda (1,500) ga jama’a da tallafin buhun Gero guda (700) ga jama’a don samun albarka.

 

Ishak Adamu ya tabbatar da cewa duk a satin daya gabata dan majalisa Garba Datti Muhammad Babawo ya saya wa hukumar kula da hadura hanya ta kasa mota ta daukar mara lafiya (ambulance)

 

“Kuma yanzu haka ya kawo wa dukkan gundumomi (11) da ake da su a fadin karamar hukumar Sabon Gari Fitillar Sola mai haske titi guda (100).”

 

Ya ce abin mamaki da alfahari shi ne da yawan aikin da shi dan majalisan ya yi a yanzu ya yi su ne bayan an shelanta ya fadi zabe duk da sun ce suna kalubalantar sakamakon zaben a matsayin an tafka magudi ne tsagwaro.

 

Malama Rukayya Muhammad daga unguwar Gabar Sabon gari tana daga cikin matan da suka sami tallafin bisa hakan, ta nuna Jin dadin horon da ta samu kuma za ta yi amfani da ilmin da ta samu kuma za yi amfani da jarin da aka ba ta domin kula da kanta.

 

Muhammad Sani daga gundumar Basawa shi ma ya sami tallafin kuma yayi wa dan majalisar fatan alheri da rokon Allah ya ba shi nasara a duk inda ya sa gabansa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsinci Gawar Wata ‘Yar Kasuwa A Otel A Jihar Oyo

Next Post

Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

Related

ÆŠan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato
Labarai

ÆŠan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

31 minutes ago
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

3 hours ago
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
Labarai

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

3 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

4 hours ago
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU
Labarai

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

5 hours ago
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

6 hours ago
Next Post
Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

Buhari Ya Yi Ta'aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
ÆŠan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

ÆŠan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

May 11, 2025
Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

May 11, 2025
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.