ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisa Ya Bayar Da Tallafi Tare Da Koyar Da Sana’o’i A Zariya

by Idris Umar
3 years ago
Zariya

Daruruwan mutane ne suka amfana da tallafi daga dan majalisa mai wakiltar karamar karamar hukumar Sabon Gari ta jihar Kaduna.

 

Tallafin da dan majalisa ya bayar ya taba bangarori da dama na rayuwar al’umar karamar hukumarsa ta Sabon Gari.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

Baya ga tallafin abinci da dan majalisa ya bayar ga darurun jama’a tuni ya shirya taron koyar da sana’ar dogaro da kai ga daruruwan jama’arsa.

 

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Wakilinmu ya ziyarci dukkan bangaren da ake bayar da horon don tabbatar wa idonsa abin da ke gudana a wajen. Wajen da ake bayar da horon ga daruruwag al’ummar ta karamar hukumar guda 2 ne kuma duk cike yake da mutane

 

Da yake zantawa da manema labarai, mai taimakawa dan majalisar a bangaren harkar gudanarwa, Kwamred Ishak Adamu (A.D.O) ya bayyana dukkan abubuwan da dan majalisan ya gudanar a ‘yan kwanakin nan wato kafin shigar watan Azumi da cikin watan azumin duk a matsayin tallafi ga jama’arsa karkashin jam’iyarsu ta APC.

 

Ishak Adamu ya ce, “A yanzu haka mutane 700 ake ba horo maza da mata da samari da har da tsofafi dukkansu ana basu horo ne na koyan kananan sana’o’i kamar yadda za su iya hada alkaki na zamani ko yadda za su hada kek na zamani kuma in sun kammala samun horon dan majalisa zai ba su naira dubu ashiri da biyar (#25,000) ga ko wanne da ya sami horon don yin jali.”

 

Mataimakin na musamman ya kara da cewa satin da ya gabata ma dan majalisar ya bayar da buhun shinkafa manya da kanana guda (1,500) ga jama’a da tallafin buhun Gero guda (700) ga jama’a don samun albarka.

 

Ishak Adamu ya tabbatar da cewa duk a satin daya gabata dan majalisa Garba Datti Muhammad Babawo ya saya wa hukumar kula da hadura hanya ta kasa mota ta daukar mara lafiya (ambulance)

 

“Kuma yanzu haka ya kawo wa dukkan gundumomi (11) da ake da su a fadin karamar hukumar Sabon Gari Fitillar Sola mai haske titi guda (100).”

 

Ya ce abin mamaki da alfahari shi ne da yawan aikin da shi dan majalisan ya yi a yanzu ya yi su ne bayan an shelanta ya fadi zabe duk da sun ce suna kalubalantar sakamakon zaben a matsayin an tafka magudi ne tsagwaro.

 

Malama Rukayya Muhammad daga unguwar Gabar Sabon gari tana daga cikin matan da suka sami tallafin bisa hakan, ta nuna Jin dadin horon da ta samu kuma za ta yi amfani da ilmin da ta samu kuma za yi amfani da jarin da aka ba ta domin kula da kanta.

 

Muhammad Sani daga gundumar Basawa shi ma ya sami tallafin kuma yayi wa dan majalisar fatan alheri da rokon Allah ya ba shi nasara a duk inda ya sa gabansa.

Zariya
Idris Umar
+ postsBio
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

MASU ALAKA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53
Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Next Post
Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

Buhari Ya Yi Ta'aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.