ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisa Ya Bayar Da Tallafi Tare Da Koyar Da Sana’o’i A Zariya

by Idris Umar
3 years ago
Zariya

Daruruwan mutane ne suka amfana da tallafi daga dan majalisa mai wakiltar karamar karamar hukumar Sabon Gari ta jihar Kaduna.

 

Tallafin da dan majalisa ya bayar ya taba bangarori da dama na rayuwar al’umar karamar hukumarsa ta Sabon Gari.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

Baya ga tallafin abinci da dan majalisa ya bayar ga darurun jama’a tuni ya shirya taron koyar da sana’ar dogaro da kai ga daruruwan jama’arsa.

 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Wakilinmu ya ziyarci dukkan bangaren da ake bayar da horon don tabbatar wa idonsa abin da ke gudana a wajen. Wajen da ake bayar da horon ga daruruwag al’ummar ta karamar hukumar guda 2 ne kuma duk cike yake da mutane

 

Da yake zantawa da manema labarai, mai taimakawa dan majalisar a bangaren harkar gudanarwa, Kwamred Ishak Adamu (A.D.O) ya bayyana dukkan abubuwan da dan majalisan ya gudanar a ‘yan kwanakin nan wato kafin shigar watan Azumi da cikin watan azumin duk a matsayin tallafi ga jama’arsa karkashin jam’iyarsu ta APC.

 

Ishak Adamu ya ce, “A yanzu haka mutane 700 ake ba horo maza da mata da samari da har da tsofafi dukkansu ana basu horo ne na koyan kananan sana’o’i kamar yadda za su iya hada alkaki na zamani ko yadda za su hada kek na zamani kuma in sun kammala samun horon dan majalisa zai ba su naira dubu ashiri da biyar (#25,000) ga ko wanne da ya sami horon don yin jali.”

 

Mataimakin na musamman ya kara da cewa satin da ya gabata ma dan majalisar ya bayar da buhun shinkafa manya da kanana guda (1,500) ga jama’a da tallafin buhun Gero guda (700) ga jama’a don samun albarka.

 

Ishak Adamu ya tabbatar da cewa duk a satin daya gabata dan majalisa Garba Datti Muhammad Babawo ya saya wa hukumar kula da hadura hanya ta kasa mota ta daukar mara lafiya (ambulance)

 

“Kuma yanzu haka ya kawo wa dukkan gundumomi (11) da ake da su a fadin karamar hukumar Sabon Gari Fitillar Sola mai haske titi guda (100).”

 

Ya ce abin mamaki da alfahari shi ne da yawan aikin da shi dan majalisan ya yi a yanzu ya yi su ne bayan an shelanta ya fadi zabe duk da sun ce suna kalubalantar sakamakon zaben a matsayin an tafka magudi ne tsagwaro.

 

Malama Rukayya Muhammad daga unguwar Gabar Sabon gari tana daga cikin matan da suka sami tallafin bisa hakan, ta nuna Jin dadin horon da ta samu kuma za ta yi amfani da ilmin da ta samu kuma za yi amfani da jarin da aka ba ta domin kula da kanta.

 

Muhammad Sani daga gundumar Basawa shi ma ya sami tallafin kuma yayi wa dan majalisar fatan alheri da rokon Allah ya ba shi nasara a duk inda ya sa gabansa.

Zariya
Idris Umar
+ postsBio
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Sanata Shehu Sani Ya Nemi Gwamnonin Arewa Su Tallafa Wa Bikin Al’adu Na ABU Zariya
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Yadda Dakta A’isha Mustapha Ta Zama Shugabar Ƙungiyar Likitocin Jihar Kaduna
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Kafafen Sadarwa Na Zamani Wuri Ne Na Bunƙasa Tattalin Arziƙi — Ubale Kiru
  • Idris Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-umar/
    Kungiyar Daliban Jami’ar ABU Ta Gudanar Gasar Girke-girken Abincin Gargajiya A Bude Bikin Al’adu Na Bana

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

Buhari Ya Yi Ta'aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.