• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kasar Brazil

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kasar Brazil
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin yau Jumma’a 14 ga wata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva, wanda har yanzu ke ziyarar aiki a kasar Sin, a babban dakin taron jama’a.

A yayin shawarwarin, Xi Jinping ya yi maraba da ziyarar Lula a kasar Sin. Ya kuma nuna cewa, kasashen Sin da Brazil su ne manyan kasashe masu tasowa, kuma muhimman kasuwanni masu tasowa a gabashi da yammacin duniya, sun kuma kasance abokan hulda bisa manyan tsare-tsare ga juna, kana suna da moriyar juna a fannoni daban daban.

  • Likitoci Sun Ja Daga A Kan Dokar Yin Aiki Na Shekara Biyar

A cewar shugaba Xi, kasar Sin na sa kaimi ga samun bunkasuwa mai inganci, da bude kofa ga waje bisa babban matsayi, wanda hakan zai kara samar da damammaki ga kasashen duniya ciki har da Brazil. Kaza lika kasar Sin tana son karfafa yin hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tare da Brazil, kan batutuwan kasa da kasa dake jawo hankulansu duka, bisa tsarin cudanyar bangarori da dama, ciki har da MDD, BRICS, da G20 da dai sauransu, tare kuma da karfafa hadin gwiwa wajen tinkarar sauyin yanayi.

A nasa bangaren kuwa, shugaba Lula ya bayyana cewa “Wannan ita ce ziyara ta farko a wata kasa da ke wajen nahiyar Amurka, tun bayan da na zama shugaban kasa a wannan karo, wanda ke nuni da irin kaunar da bangaren Brazil ke da shi ga kasar Sin, da kuma muhimmancin da yake ba wa ci gaban dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, kasarsa ta kuduri aniyar bunkasa huldar kut da kut da kasar Sin bisa matsayin manyan tsare-tsare na sa kaimi ga kafa tsarin kasa da kasa mai adalci da ma’ana.

Bayan shawarwarin, shugabannin kasashen biyu sun shaida rattaba hannu kan wasu takardu na hadin gwiwa da suka shafi kasuwanci da zuba jari, da tattalin arziki na zamani, da kirkire-kirkire na kimiyya da fasaha, da watsa labarai da sadarwa, da rage talauci, da binciken annoba da kuma sararin samaniya da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Bugu da kari, bangarorin biyu sun kaddamar da “Sanarwar hadin gwiwa tsakanin Jamhuriyar Jama’ar Sin da Jamhuriyar Tarayyar Brazil, kan zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni.” (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babbar Jami’Ar IMF: An Hasashen Cewa Sin Za Ta Ba Da Gudummawar Kusan Kashi 1bisa 3 Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya A Bana

Next Post

Hukunce-Hukuncen Sallar Idi Da Zakatul Fidir

Related

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

38 minutes ago
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

2 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

3 hours ago
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

24 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

1 day ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

1 day ago
Next Post
Hukunce-Hukuncen Sallar Idi Da Zakatul Fidir

Hukunce-Hukuncen Sallar Idi Da Zakatul Fidir

LABARAI MASU NASABA

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridan Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridan Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

October 5, 2025
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.