• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa Ya Haifar Da Hargitsi A Kasar Sudan?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wa Ya Haifar Da Hargitsi A Kasar Sudan?

LONDON, UNITED KINGDOM - 2021/10/30: A protester holds a 'Save Sudan' placard during the demonstration. Large crowds gathered outside Downing Street in protest against the military coup in Sudan and demanding a return to civilian rule. (Photo by Vuk Valcic/SOPA Images/LightRocket via Getty Images)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tashin hankalin da ya abku a kasar Sudan a kwanakin nan ya ja hankalin mutanen duniya. Inda labaran da aka watsa suka nuna cewa wannan rikici ne da ake samu tsakanin shugabannin sojoji na tsagi daban daban.

Sai dai idan an bi bahasin ainihin dalilin abkuwar lamarin, to, za a gano cewa, kasar Amurka da yadda take shisshigi a harkokin gidan kasar Sudan su ne suka haifar da yamutsi a kasar.

  • Buhari Ya Damu Kan Yadda Rikici Ya Barke A Sudan

Manyan jami’an da suke rikici da juna a wannan karo a kasar Sudan, wato Abdel al-Burhan, kwamandan rundunar sojojin kasar, da Mohamed Dagolo, madugun rundunar RSF, sun kwaci ikon mulki daga hannun Omar al-Bashir, tsohon shugaban kasar, ta hanyar aiwatar da juyin mulki a hadin gwiwarsu, a shekarar 2019, inda suka samu goyon baya daga kasar Amurka.

Idan mun duba tarihin shisshigin kasar Amurka a kasar Sudan, za mu ga ya fara ne tun farkon mulkin shugaba Omar al-Bashir a Sudan, inda a farkon shekarun 1990, kasar Amurka ta gabatar da kara ga babban taron Majalisar Dinkin Duniya cewar Sudan na keta hakkin dan Adam, sa’an nan kasar ta sa kasashe daban daban daina samar da agaji ga kasar Sudan.

Zuwa shekarar 1993, hukumar lamuni ta duniya IMF ta sanya kasar Sudan cikin jerin kasashen da suka kasa biyan basusukan da ake binsu, da dakatar da ikonta na jefa kuri’a a matsayin daya daga cikin mambobin hukumar, duk bisa umarnin da kasar Amurka ta gabatar. Dai dai a wannan shekara kuma, kasar Amurka ta sanya Sudan cikin jerin kasashen da suke “marawa ta’addanci baya”, da fara saka takunkumi kan kasar a shekarar 1996. Bayan haka, kasar Amurka ta taba hana kasar Sudan halartar takarar neman kujerar kwamitin sulhu na MDD da ba ta dindindin ba, da haifar da matsala ga kasar Sudan a kokarinta na fitar da danyen mai don samun kudi, gami da hana ta sayen makamai daga sauran kasashe, da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Da ma kasar Sudan wata kasa ce da ta mallaki dimbin albarkatun mai, da ma’adinai iri daban daban, da sauran albarkatun da ake bukata wajen raya masana’antu, amma takunkumin da aka saka mata cikin wani dogon lokaci ya hana kasar samun ci gaban tattalin arziki. Har yanzu kasar na dogaro kan aikin noma, kuma ba shi da karfin masana’antu. Alkaluman da aka samu daga hukumar IMF sun nuna cewa, kashi 47% na mutanen kasar na fama da talauci.

Ban da wannan kuma, mulkin mallaka da ‘yan kasar Birtaniya suka yi a kasar Sudan ya haifar da wani yanayi mai sarkakiya a kasar, a fannin kabilu da addinai. Sa’an nan kasar Amurka ta yi amfani da wannan yanayi wajen samar da goyon baya ga bangarori masu adawa da gwamnati dake Sudan, abun da ya sa ake yawan samun tarzoma a kasar.

A yankin Darfur dake yammacin kasar Sudan, an dade ana samun rikicin kabilu da shisshigi daga makwabtan kasashe, lamarin da ya haifar da matsalar jin kai mai tsanani. Sai dai kasar Amurka ta yi amfani da wannan dama wajen samar da makamai ga dakarun yankin masu adawa da gwamnati, gami da zargin gwamnatin kasar Sudan da keta hakkin dan Adam yayin da take neman daidaita maganar Darfur, kuma ta saka wa kasar takunkumi bisa wannan dalili.

Ban da wannan kuma, an taba samun dimbin albarkatun mai a kudancin kasar Sudan, inda dakarun wasu kabilu suka nemi a ba su ikon cin gashin kai. Daga bisani, a shekarar 2011, kasar Amurka ta hurewa kabilun kudancin kasar Sudan kunne, domin su balle yankin daga kasar, da kafa kasar Sudan ta Kudu, ta yadda wannan sabuwar kasa ta zama karkashin sarrafawar kasar Amurka din.

Wannan lamari ya sa kasar Sudan rashin kashi 70% na albarkatun mai, da fuskantar raguwar kudin shiga, da tsanantar yanayin koma bayan tattalin arziki, abun da ya sa dimbin jama’ar kasar aiwatar da zanga-zanga a wurare daban daban sakamakon matukar fushi. Daga baya, bisa goyon bayan da kasar Amurka ta bayar, Abdel al-Burhan da sauran manyan hafsoshin rundunar sojan kasar suka kaddamar da juyin juya hali, wanda ya kai ga hambarar da shugaba Omar al-Bashir, a shekarar 2019.

Sai dai ko da yake an kifar da “mai mulkin zalunci”, kamar yadda kasar Amurka ta fada, ana ci gaba da fama da tashin hankali a kasar Sudan. Wani lokaci bangaren sojojin kasar ya ki mika mulki ga jami’ai, wani lokaci ma ake samun ja-in-ja tsakanin rukunoni dake cikin sojojin kasar. Zuwa yanzu wannan yanayi na sa kafar wando daya ya zama wani babban tashin hankali mai tsanani. Ta wannan ana iya ganin cewa, duk wani wurin da kasar Amurka ta yi shissigi, ba za a rasa rikici da yamutsi ba.

Ban da wannan kuma na tuna da wani labarin da na gani a watan da ya gabata, inda mista Dai Bing, mukaddashin wakilin tawagar kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya, ya yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar da ya soke takunkumin da aka sanya wa kasar Sudan. Ya ce, “ Yanayin da ake ciki a yankin Darfur ya riga ya daidaita sosai, don haka ci gaba da saka ma kasar Sudan takunkumi ba shi da ma’ana a dukkan bangarorin siyasa da tsaro, kawai an haifar da matsala ga yunkurin gwamnatin Sudan na tabbatar da tsaro.” Sai dai “wasu mambobin kwamitin sulhu” ba su son soke takunkumin, maimakon haka suna neman sanya matakin ya dauwama. Ma iya cewa, wasu kasashe ba su son ganin kasashen Afirka sun samu damar raya kansu ko kadan.

A cikin watan Ramadan mai tsarki, ina so ku taya mu addu’ar samun dawowar zaman lafiya.

Da fatan wata rana kasar Sudan da wasu kasashen dake nahiyar Afirka za su magance shisshigin da ake musu tun da wuri, da samun cikakkun damammaki na yanke shawara bisa ra’ayinsu, da hadin kai, da kuma samun ci gaba. Wannan rana za ta zo, illa dai jama’ar kasashen Afirka su fahimci ainihin burin masu neman yin shisshigi a harkokin sauran kasashe, wato ta da rikici, da haifar da matsala. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Fintiri Ya Kayar Da Binani A Kujerar Gwamnan Adamawa

Next Post

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 28

Related

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

1 hour ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

2 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

4 hours ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

24 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

1 day ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

1 day ago
Next Post
Ramadan

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 28

LABARAI MASU NASABA

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.