Rundunar ‘Yansndan Jihar Kwara ta ceto mutane uku da aka yi garkuwa da su a yankin Igbonla da ke kudancin jihar.
‘Yansandan sun ce, wadanda aka ceto sun hada da Kudus Wasiu, Fatima Wasiu da ‘yarta ‘yar wata shida.
ADVERTISEMENT
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, Toun Ejire – Adeyemi, a cikin wata sanarwa a ranar Talata, ya ce, ana ci gaba kuma da kokari don ceto sauran mutane biyu – Wasiu Salihu, Abdullahi Sefiu; da kuma kama cafke maharan.














