• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hare-haren Bindiga Da Ke Hallaka Amurkawa Na Shaida Gazawar Gwamnati Wajen Kare Hakkin Bil Adama

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hare-haren Bindiga Da Ke Hallaka Amurkawa Na Shaida Gazawar Gwamnati Wajen Kare Hakkin Bil Adama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokai, a karshen makon da ya gabata, fararen hular kasar Amurka sun sha fama da harbe-harben bindiga, wanda hakan ya haifar da asarar rayuka da dama. Bisa labarin da aka bayar, a daren ranar 15 ga watan nan, an samu aukuwar harin bindiga a garin Dadeville na gabashin jihar Alabama, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane a kalla 4, baya ga sauran wasu 28 da suka ji rauni.

Baya ga haka, a wannan rana, an fuskanci hare-haren bindiga a wata jami’a dake kudu maso gabashin jihar Pennsylvania, da wani lambun shan iska dake birnin Louisville na jihar Kentucky, hare-haren da suka yi sanadin mutuwar mutane 2 da jikkatar wasu 4.

  • Matsakaiciyar Karuwar Sana’ ar Manhajoji A Sin Ta Kai Kaso 16% Duk Shekara

Bisa kididdigar da shafin intanet na Gun Violence Archive ya bayar, tun farkon wannan shekara zuwa yanzu, an samu aukuwar hare-haren bindiga a wuraren da jama’a ke taruwa har sau 163, lamarin da ya haifar da rasuwar mutane fiye da dubu 12.

A hannu guda kuma, kungiyar masu rajin kare mallakar bindiga ta Amurka ta NRA, ta gudanar da taron shekara-shekara a ran 14 ga watan nan, a birnin Indianapolis na jihar Indiana, bikin da masu goyon bayan mallakar bindiga da dama suka halarta, ciki har da wasu manyan jami’an jam’iyyar Republican wadanda suka bayyana goyon bayansu ga NRA.

A daya bangaren kuma, cibiyar dake rajin kare dokar hana hare-haren bindiga ta Giffords dake kasar Amurka, ta fitar da rahoto dake cewa, NRA mai mambobi fiye da miliyan 5 da kudade masu dimbin yawa, na da babbar alaka da harkokin siyasa da suka shafi zabuka a kasar, kuma hakan ya sa ‘yan siyasa ke dora muhimmanci sosai a kan kungiyar.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Cibiyar ta kara da cewa, yayin da ‘yan siyasar Amurka ke ja-in-ja da juna kan batun mallakar bingida, fararen hula ne kawai suke daukar asara.

Gwamnatin Amurka wadda ake jinjinawa da sunan “Mai kare hakkin Bil Adama”, mutuncinta ya zube, sakamakon yawan aukuwar hare-haren bindiga dake addabar al’ummar kasar. (Mai zane da rubuta: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Gabon

Next Post

Karamar Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ba Da Hutun Ranar 21 Da 24 Ga Afrilu

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

27 minutes ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

31 minutes ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

2 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

4 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

4 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

6 hours ago
Next Post
Karamar Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ba Da Hutun Ranar 21 Da 24 Ga Afrilu

Karamar Sallah: Gwamnatin Tarayya Ta Ba Da Hutun Ranar 21 Da 24 Ga Afrilu

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.