• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wanda Zai Iya Rushe Masarautun Kano, Martanin Ganduje Ga Kwankwaso

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babu Wanda Zai Iya Rushe Masarautun Kano, Martanin Ganduje Ga Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya sake nanata cewa sabbin masarautu hudu da gwamnatinsa ta kirkiro suna nan daram.

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Litinin yayin bikin ranar ma’aikata da aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano.

  • An Kwaso Daukacin Daliban Nijeriya Da Suka Makale A Khartoum – Kungiyar Dalibai
  • Gwamnatin Edo Za Ta Kashe Naira Biliyan 6 Wajen Gyaran Makarantun Sakandare A Jihar 

Kalaman nasa na zuwa ne kwanaki kadan bayan da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana a wani faifan bidiyo cewa gwamnatin Abba Yusuf mai jiran gado za ta sake duba salon mulkin masarautun Kano.

Sai dai Gwamna Ganduje wanda ya raba masarautun Kano gida biyar sannan ya tsige Sarkin Kano Muhammadu Sunusi na wancan lokacin ya bayyana cewa sabbin masarautun guda hudu alama ce ta hadin kai, ci gaba da jin dadin al’umma.

Ya kara da cewa an kirkiro masarautun ne domin karrama al’ummar yankunan da kuma dawo da martabar masarautun gargajiya.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

“Duk wanda ya ziyarci hedikwatar wadannan sabbin masarautun zai yarda cewa mun kawo ci gaba a wadannan wuraren. Mun kirkire su ne domin karrama mutanen wadannan yankuna,” in ji Ganduje.

Ya kuma tabbatar wa da al’ummar Kano cewa masarautu na dindindin ne kuma sun zo su zauna, ya kuma kara da cewa duk wanda ya yi yunkurin rusa su Allah ba zai kawo shi Jihar Kano ba.

“Ko ba ma gwamnati muna addu’a kuma za mu ci gaba da addu’ar Allah ya kare wadannan masarautun daga dukkan sharri. Na gode muku duka,” in ji shi.

Samar da sabbin masarautun dai ya kasance batun cece-kuce a Kano tun daga 2020, inda wasu ke goyon bayan matakin yayin da wasu ke adawa da shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaGandujegwamnatikanoKwankwasoMasarautu
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Riƙa Tabbatar Da Hukunci Ga Masu Yaɗa Labarun Ƙanzon Kurege – CI Sunday James

Next Post

Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

15 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

24 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

LABARAI MASU NASABA

Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.