• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai ‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 13 Da Ke Da Asusun Banki Ba Su Da BVN, In Ji CBN

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A Nijeriya an yi hasashen cewa akwai kimanin mutum miliyan 200 na yawan ‘yan kasar, an bayyana cewa a cikin wadannan adadi akwai sama da mutum miliyan 70 da ke da asusun banki a bankunan kasuwancin Nijeriya.

Cikin wadannan suke da asusun bankin, akwai ‘yan Nijeriya sama da miliyan 57 da ke da asusun banki kuma suna da lambar BVN, sai dai akwai sama da ‘yan Nijeriya 13 da suna amfani da asusun banki amma ba su da BVN.

  • Kwastam Ta Kama Kayan Miliyan 55 A Adamawa

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi hadin gwiwa da hukumar daidaita alaka a tsakanin bankunan Nijeriya (NIBSS) da kwamitin masu bankuna da kuma masu ajiya a bankuna domin kaddamar da aikin samar da lambar BVN a watan Fabrairun 2014.

An kirkiro lambar BVN ne ga masu mu’amula da bankunan Nijeriya domin tantance su wajen rage damfarar kudade da inganta gudanar da ayyukan bankuna a kasar.

Tun bayan bullo da lamarin, BVN ya kasance yana da matukar muhimmin wajen abubuwan da ake bukata don budewa da kuma kula da asusun banki a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ne ya bayyana haka a birnin Kalaba wajen taron kara wa juna sani karo na 34 na masu aiko da rahotannin kudade da kuma editocin harkokin kasuwanci.

Emefiele wanda ya samu wakilcin Daraktan Sashen Kayyade Kudade na CBN, Dakta Hassan Mahmoud ya ce, “Har a zuwa ranar 31 ga Maris ta 2023, jimillar wadanda suke da BVN a Nijeriya guda 57,431,355, kuma BVN yana taimakawa wajen bunkasa harkokin ijiya a bankuna, wanda hakan zai taimaka don inganta damar samun rance ga masu karbar bashin bankuna.”

Gwamnan CBN ya kara da cewa BVN zai ci ci gaba da zama lambar tantance asusun banki da ke bukatar a matsayin wani bangare na shirye-shiryen saukaka wahalhalun da ke tattare da rashin tantance kwastomomin bankuna.

Ya ce CBN zai ci gaba da tallafa wa kwastomomin banki da ba su BVN domin su mallaki lambar ta saukakkiyar hanya.
Emefiele ya kara da cewa an gabatar da tsarin biyan kudi na PSB 2025 domin fadada hanyoyin biyan kudade ga abokan ciniki da kuma karfafa kula da tsarin biyan kudi.

Da yake karin haske game da tsarin biyan kudin, gwamnan CBN ya bayyana cewa babban bankin yana amfani da tsarin biyan kudi a matsayin wata hanyar samun nasara a harkokin kudade da kasar nan ta saka a gaba.

Bincike ya nuna cewa kashi 34 ne na ‘yan Nijeriya ke da asusun banki, kuma kashi 9 ne kacal ke iya gudanar da hada-hadar kudade ta hanyar fasahar zamani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tataburzar Hana Shigo Da Taliyar ‘Yan Yara Daga Waje Za Ta Zama Alheri Ga Nijeriya

Next Post

Tinubu Zai Fuskanci Bore Kan Tsayar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisa Da Tajudden A Matsayin Kakaki

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

3 hours ago
BVN
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

12 hours ago
Next Post
Tinubu Zai Fuskanci Bore Kan Tsayar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisa Da Tajudden A Matsayin Kakaki

Tinubu Zai Fuskanci Bore Kan Tsayar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisa Da Tajudden A Matsayin Kakaki

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
BVN

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.