ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai ‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 13 Da Ke Da Asusun Banki Ba Su Da BVN, In Ji CBN

by Sulaiman
3 years ago
Noma

A Nijeriya an yi hasashen cewa akwai kimanin mutum miliyan 200 na yawan ‘yan kasar, an bayyana cewa a cikin wadannan adadi akwai sama da mutum miliyan 70 da ke da asusun banki a bankunan kasuwancin Nijeriya.

Cikin wadannan suke da asusun bankin, akwai ‘yan Nijeriya sama da miliyan 57 da ke da asusun banki kuma suna da lambar BVN, sai dai akwai sama da ‘yan Nijeriya 13 da suna amfani da asusun banki amma ba su da BVN.

  • Kwastam Ta Kama Kayan Miliyan 55 A Adamawa

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yi hadin gwiwa da hukumar daidaita alaka a tsakanin bankunan Nijeriya (NIBSS) da kwamitin masu bankuna da kuma masu ajiya a bankuna domin kaddamar da aikin samar da lambar BVN a watan Fabrairun 2014.

ADVERTISEMENT

An kirkiro lambar BVN ne ga masu mu’amula da bankunan Nijeriya domin tantance su wajen rage damfarar kudade da inganta gudanar da ayyukan bankuna a kasar.

Tun bayan bullo da lamarin, BVN ya kasance yana da matukar muhimmin wajen abubuwan da ake bukata don budewa da kuma kula da asusun banki a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ne ya bayyana haka a birnin Kalaba wajen taron kara wa juna sani karo na 34 na masu aiko da rahotannin kudade da kuma editocin harkokin kasuwanci.

Emefiele wanda ya samu wakilcin Daraktan Sashen Kayyade Kudade na CBN, Dakta Hassan Mahmoud ya ce, “Har a zuwa ranar 31 ga Maris ta 2023, jimillar wadanda suke da BVN a Nijeriya guda 57,431,355, kuma BVN yana taimakawa wajen bunkasa harkokin ijiya a bankuna, wanda hakan zai taimaka don inganta damar samun rance ga masu karbar bashin bankuna.”

Gwamnan CBN ya kara da cewa BVN zai ci ci gaba da zama lambar tantance asusun banki da ke bukatar a matsayin wani bangare na shirye-shiryen saukaka wahalhalun da ke tattare da rashin tantance kwastomomin bankuna.

Ya ce CBN zai ci gaba da tallafa wa kwastomomin banki da ba su BVN domin su mallaki lambar ta saukakkiyar hanya.
Emefiele ya kara da cewa an gabatar da tsarin biyan kudi na PSB 2025 domin fadada hanyoyin biyan kudade ga abokan ciniki da kuma karfafa kula da tsarin biyan kudi.

Da yake karin haske game da tsarin biyan kudin, gwamnan CBN ya bayyana cewa babban bankin yana amfani da tsarin biyan kudi a matsayin wata hanyar samun nasara a harkokin kudade da kasar nan ta saka a gaba.

Bincike ya nuna cewa kashi 34 ne na ‘yan Nijeriya ke da asusun banki, kuma kashi 9 ne kacal ke iya gudanar da hada-hadar kudade ta hanyar fasahar zamani.

BVN
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Next Post
Tinubu Zai Fuskanci Bore Kan Tsayar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisa Da Tajudden A Matsayin Kakaki

Tinubu Zai Fuskanci Bore Kan Tsayar Da Akpabio A Matsayin Shugaban Majalisa Da Tajudden A Matsayin Kakaki

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.