• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ba Ta Da Lokacin Sa-In-Sa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Kasar Sin
0
Kasar Sin

Sin da Gabon sun daga matsayin dangantakarsu zuwa cikakkiyar dangantakar abokantaka ta hadin

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan, an jiyo wasu kusoshin gwamnatin Amurka na yawaita korafi, game da abun da suka kira “watsin da Sin ke yi da batun tattanawa da tsagin Amurka”. Cikin irin wadannan zarge-zarge, an jiyo wasu ’yan siyasar kasar na zargin cewa wai “Sin ta ki tsayar da sabon lokacin da ya dace sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya gudanar da ziyara a Sin”. Har ila yau, tsagin Amurka ya yi zargin cewa, ma’aikatar tsaron Sin ta ki ta amince da bukatar ma’aikatar tsaron Amurka na zantawa, yayin da kuma ministocin tsaron kasashen biyu suka shafe tsawon kusan watanni 5 ba su zanta da juna ba.

Bugu da kari, a yayin taron ministocin wajen kasashe mambobin kungiyar G7 da ya gudana a ’yan kwanakin baya a kasar Japan, an jiyo ministan harkokin wajen Amurka Antony Blinken na kira ga kasar Sin, da ta fayyace matsayarta game da alakarta da Amurka. Kana a cewarsa, sauran kasashen duniya na zuba ido don ganin sassan biyu sun daidaita alakarsu ta hanyar nuna sanin ya kamata.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Karfin Tattalin Arzikin Kasar Zai Ci Gaba Da Taimakawa Murmurewar Tattalin Arzikin Duniya

To amma abun tambaya a nan shi ne, yayin da ake kokarin raya dangantakar kasashe daban daban, bangare daya ne ya dace ya nuna sanin ya kamata? Tabbas kowa ya san cewa “Ana iya kai Doki bakin ruwa, amma ba za a iya tilasa masa shan ruwa ba”. Ga misali, Amurka ce ta dage ziyarar da Mr. Blinken ya shirya kaiwa kasar Sin a watan Fabarairu, biyowa bayan surutai da suka rika bazuwa, game da harbo balan balan din nan ta kasar Sin da Amurka ta yi, kuma hakan ya auku ne daf da lokacin da Blinken din ke shirin tashi daga Amurka zuwa Sin.

Idan mun yi duba na tsanaki za mu ga cewa, Amurka ce ta dakatar da waccan ziyara bisa radin kanta, amma a yanzu take kokarin nunawa duniya tamkar Sin ce ke da alhakin dakatar da zuwan nasa. Wata tambayar ta daban ita ce, shin zai yiwu komai ya zama daidai da ra’ayin Amurka, kuma sai dai kowa ya bi ra’ayin ta yayin da ake hadin gwiwa?

Ko shakka babu kasar Sin babbar kasa ce dake da tarin hidimomin wanzar da ci gaban kanta, da ma kyautata hadin gwiwa da kasashen da suka rungumi tafiya irinta, don haka ba ta da lokacin batawa, ko shiga cacar baka, ko cece-kuce da wata kasa. Kaza lika salon diflomasiyyar kasar Sin na cike da muhimman ayyuka, wadanda ba zai yiwu a samu wata kafa ta biyewa bukatun Amurka ba, musamman ma batun da ya shafi shirya wata ziyara ga mutane masu kunbiya-kunbiya, ko wata boyayyar manufa.

Labarai Masu Nasaba

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

Game da dalilin da ya sanya ministocin tsaron Sin da Amurka suka kwashe tsawon lokaci ba su zanta da juna ba kuwa, Amurka ta fi kowa sanin dalili, domin kuwa har yanzu ba ta janye takunkumai na rashin adalci da ta kakabawa sabon ministan tsaron kasar Sin janar Li Shangfu ba. Wanda hakan ya haifar da rashin kyakkyawan yanayi, da zai ba da damar tattaunawa tsakanin jami’an sojin kasashen biyu yadda ya kamata. Don haka idan har Amurka na son zantawa, ko tattaunawa da tsagin kasar Sin, to bai kamata ta dauki irin wannan mataki na raba gari ba.

Kasar Sin
Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” ta zama Hantsi leka gidan kowa

Wani abun lura ma shi ne ita kanta Amurka, ta ganewa idanunta yadda a cikin watannin baya bayan nan, jagororin kasashe da dama, ciki har da na kawayenta, da shugabannin wasu hukumomin kasa da kasa suka rika ziyartar kasar Sin, tare da cimma kyakkyawan sakamako. Don haka abun tambayar a nan shi ne, me ya sa ake samun matsala da Amurka ita kadai a wannan fage?

Sinawa su kan ce “Saurari kalaman su ka kuma lura da ayyukan su”. To sai dai fa game da Amurka ta yau, kusan ma bata lokaci ne sauraren kalamanta, duba da yadda take furta maganganu tare da warware su ta hanyar aiwatar da matakai da suka saba da furucin nata. Don haka ana iya cewa, kalaman Amurka sun rasa kimarsu a idanun kasar Sin, da ma da yawa daga bangarorin kasa da kasa.

Kasar Sin
Sin da Amurka na bukatar kyautata alaka domin cimma moriyar juna da bunkasa ci gaban duniya baki

A baya bayan nan ma wasu rahotanni daga wasu kafofin watsa labaran Amurka, sun bayyana shirin gwamnatin kasar mai ci na aiwatar da wasu sababbin dokoki, wadanda a karkashinsu za ta tilastawa Amurkawa masu zuba jari, takaita yawan jarin da za su iya zubawa a kasar Sin. A hannu guda kuma, Amurka na kara tsoma baki cikin batun yankin Taiwan ba ji ba gani. Don haka ana iya cewa, matakan Amurka na kokarin dakile, ko mayar da kasar Sin baya na kara tsananta.

Duniya dai na ganin yadda kalaman jagororin Amurka ke sabawa ayyukan ta musamman game da batutuwan da suka shafi kasar Sin. Don haka zai yi wuya Sin ta amince da alkawuran dake fitowa daga bakin makusantan gwamnatin Amurka.

Ko shakka babu tattaunawa da cudanya suna iya bunkasa hadin gwiwa, kana suna yaukaka alakar sassa daban daban, kuma matakai ne na kandagarkin barkewar rikici ko takaita sabani. To sai dai kuma a bangaren ta, Washington tana boye manufarta karkashin wadannan kyawawan matakai, inda take son cimma moriyar siyasa ta hanyar abun da take kira “Tattaunawa da bangaren Sin”.

Kasar Sin
Duk tsananin sabani Sin da Amurka na bukatar juna

A nata bangaren kuwa, har kullum kasar Sin na daukar cudanyar ta da tsagin Amurka a matsayin wata babbar dama, ta kyautata dangantaka bisa hakuri da juriya, wanda hakan shi ne nauyin da Sin din ta runguma a matsayin ta na babbar kasa. Har ila yau, Sin na goyon bayan tattaunawa, da musaya bisa martaba juna, da rungumar matakan zaman lafiya, da hadin gwiwar cimma moriya tare, ta yadda za a kai ga yaukaka dangantakar Sin din da Amurka lami lafiya. Sai dai kuma akasari, shaidu na zahiri na nuna cewa, bukatar Amurka ta yin cudanya da Sin batu ne kawai na fatar baki, wanda take amfani da shi wajen jawo ra’ayi, da samun yardar kawayenta, da sauran kasashen da suke nuna matukar damuwa ga yanayin tabarbarewar alakar sassan biyu, yayin da a daya hannun Amurkan ke amfani da hakan wajen shafawa Sin kashin kaji.

Sanin kowa ne cewa, a shekarun baya bayan nan, ana ta fuskantar yanayi na rashin tabbas da kalubaloli daban daban a duniya, ta yadda hadin kai da cimma moriyar juna ya zama burin dukkanin kasashen duniya. Kaza lika sassan kasa da kasa sun fahimci cewa, kulla kawance da zai kare muradun kashin kai, ko katse hulda da wasu sassa, ko yakin cacar baka, ba za su haifarwa kowa da mai ido a yanayin da ake ciki ba. Shi yasa kasashen duniya daban daban ke kara rungumar tafiyar kasar Sin, duba da yadda take ta kara bude kofofin ta ga kasashen waje, da ci gaban da take samu tare da abokan huldar ta a bangarori daban-daban.

A baya bayan nan mun ga yadda shugabannin kasashe da dama ke ta kara amincewa da makomar hadin kansu da kasar Sin, matakin dake kara haifar musu da alherai masu tarin yawa.

Idan muka waiwayi tarihi, za mu ga tun bayan kafuwar janhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, Sin ba ta taba ruwa wutar yaki to haifar da hatsaniya ba, kana bata taba amfani da karfi domin mallakar wani yanki da ba nata ba. Kuma har zuwa yau, Sin ce kasa daya tilo a duniya, da ta sanya manufar samun ci gaba ta hanyar lumana cikin kundin tsarin mulkin ta.

Har kullum, burin kasar Sin shi ne martaba ikon mulkin kai, da ikon kasashe na kare cikakkun yankunan su. Kaza lika kasar Sin na matukar adawa da tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe na daban. Sabanin haka kuwa, wasu kasashen yammacin duniya na ganin duk wata kasa da ta samu ci gaba, akwai yiwuwar ta yi amfani da tasirin ta wajen yin babakere da nuna fin karfi.

Kasar Sin
Me ya sa har kullum Amurka ke da wuyar cimma daidaito

Shaidu na zahiri sun nuna cewa, burin kasar Sin shi ne tabbatar da ci gaban duniya baki daya, a matsayin wani makami na warware dumbin matsaloli masu sarkakiya da bil adama ke fuskanta, kuma hakan ne ya sa Sin din ke sa kaimin yin hadin gwiwa da dukkanin kasashe, bisa shawarar nan ta “Ziri Daya Da Hanya Daya”, ta kuma gabatar da shawarar raya duniya baki daya.

Wani hasashe ma na bankin duniya ya nuna cewa, idan har aka yi nasarar aiwatar da dukkanin shirye-shirye na gina ababen more rayuwa ta fannin sufuri, karkashin shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”, ya zuwa shekarar 2030, hakan zai rika samar da kudaden shiga har dalar Amurka tiriliyan 1.6 a kowace shekara, yayin da kuma kasashen da suka rungumi shawarar za su ci gajiyar kimanin kaso 90 bisa dari na kudaden. Don haka dai muna iya cewa, bunkasuwar kasar Sin, dama ce ga kowa ba wai kalubale ba!

Alal hakika, kyautata hulda tsakanin Sin da Amurka, mataki ne da zai inganta moriyar kasashen biyu, zai kuma haifar da kwanciyar hankali da bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya. Kuma ko kadan, Sin ba abokiyar gabar Amurka ba ce. Don haka kamata ya yi a yi watsi da ra’ayin yakin cacar baka, ko burin cin nasara daga hasarar wani bangare, maimakon hakan, ya dace sassan biyu su kyautata huldar su bisa turbar zaman lafiya da lumana. Kuma ko shakka ba bu wannan ita ce matsayar kasar Sin.

Ana iya ganin hakan a zahiri, idan aka dubi yadda kasar Sin ta karbi bakuncin shugabannin duniya da dama a ‘yan makwannin baya bayan nan, ciki har da shugaban kasar Gabon Ali Bango Ondimba, wanda a yayin ziyarar sa a Sin, shi da shugaba Xi Jinping suka amince da kudurin daga matsayin cikakkiyar dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashen su, zuwa cikakkiyar dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare.

Kafin ziyarar shugaban na Gabon, Sin ta karbi bakuncin shugabannin kasashen Faransa, da na Brazil, da shugabar tarayyar Turai, baya ga firaministocin kasashen Sifaniya, da Malaysia, da Singapore. Kaza lika a baya bayan nan shugaba Xi Jinping ya zanta ta watar tarho da shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy, inda suka yi musayar ra’ayi game da halin da ake ciki don gane da rikicin kasar ta Ukraine, da ma yadda ya dace a shawo kan rikicin bisa turbar diflomasiyya.

Daga karshe, wasu masharhanta na ganin jan kafar da Amurka ke yi game da batun hawa teburin shawara ba wani abun damuwa ba ne, domin kuwa, har kullum kofofin kasar Sin a bude suke, kuma duk lokacin da Amurka ta nuna hali na dattaku, ta aiwatar da matakai na zahiri, abu ne mai sauki a koma kan teburin shawara, da musayar ra’ayoyi a fannoni daban daban tsakanin ta da Sin, wanda hakan ne hakikanin burin kasashen duniya game da alakar sassan biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Karfin Tattalin Arzikin Kasar Zai Ci Gaba Da Taimakawa Murmurewar Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Shekara 61 Da Haihuwar Sam Nda-Isaiah: Waiwayen Mukarrabai Kan Mashahuran Hikimominsa

Related

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
Daga Kasar Sin

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

3 months ago
Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin
Daga Kasar Sin

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

11 months ago
wang lili
Daga Kasar Sin

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

11 months ago
Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura
Daga Kasar Sin

Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura

1 year ago
Zambiya
Daga Kasar Sin

’Yar Kasar Zambiya: A Nan Kasar Sin, Ina Jin Tamkar Ina Gida!

1 year ago
Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin
Daga Kasar Sin

Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin

1 year ago
Next Post
Sam Nda-Isaiah

Shekara 61 Da Haihuwar Sam Nda-Isaiah: Waiwayen Mukarrabai Kan Mashahuran Hikimominsa

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.