• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin, Kyakkyawar Fata Ga Makomar Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin, Kyakkyawar Fata Ga Makomar Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin za ta jagoranci taro kai tsaye na farko cikin shekaru 31 tsakaninta da kasashen yankin tsakiyar Asiya da suka hada da Kazakhstan da Kyrgystan da Tajikistan da Turkmenistan da Uzbekistan, a ranakun 18 da 19 ga wata, wanda ke zaman muhimmin taro tsakanin bangarorin.

A ganina, wannan taro zai kara tabbatar da karfin kasar Sin na jagorantar kasashe masu tasowa wajen samun ci gaban da suke muradi da kuma ba su damar shiga ana damawa da su cikin harkokin kasa da kasa.

  • Karuwar Cinikin Wajen Sin A Watanni 4 Na Farkon Bana Ta Kai Kaso 5.8 Bisa Dari Kan Na Makamancin Lokaci Na Bara

Hakika ba al’ummar kasar Sin ne kadai ke amfana da ci gaban da kasar ta samu ba, har ma da kasashe masu tasowa, inda take fito da su tare da kara sanyawa ana jin amonsu, domin in ban da kasar Sin, babu wata babbar kasa dake kokarin jan kasashe masu tasowa a jiki da zuciya daya.

Tarihi ya nuna cewa, kasar Sin na daya daga cikin kasashen da suka fara kulla huldar diflomasiyya da wadannan kasashe tun bayan samun ’yancin kansu, kuma tun daga lokacin ake samun kyautatuwar alaka a tsakaninsu.

Hakika hulda da kasar Sin babban tagomashi ne ga kowace kasa domin ta kasance mai tabbatar da adalci da aiwatar da dangantaka bisa girmama juna da moriyar juna, da kuma kaunar ganin an gudu tare an tsira tare. Burin kasar Sin a kullum shi ne ganin ci gaban kasashe masu tasowa, da burin ganin sun tsaya da kafarsu sun kuma nemi ci gaba ta hanyar da ta dace da su. Irin wannan ra’ayi shi ne ya dace da kyautata zaman lafiya da ci gaban duniya da ma kyautata zamantakewar al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Yayin da wasu kasashe suka dukufa wajen yin babakere da tsoma baki da neman ci da gumin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta kasance wata sabuwa kuma kyakkayawar fata ga makomar kasashe masu tasowa.

Bugu da kari, dangantakar wadannan kasashe za ta taimaka wajen kyautata zaman lafiyar yankin Asiya. Dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya, dangantaka ce ta moriyar juna bisa la’akari da hadin gwiwarsu a bangarori kamar na makamashi da fasaha da hakar ma’adinai da amfanin gona, inda kayayyakin wadannan bangarori da Sin ta shigo da su daga wadannan kasashe a bara, suka kasance mafi yawa, haka kuma su ne suka fi sayen kayayyakin laturoni da injuna daga kasar Sin.

Lamarin da ke nuna cewa, taron dake karatowa, zai kara bunkasa kyakkyawar dangantakar dake akwai tsakaninsu, tare da samar da karin sabbin damarmaki da ci gaban tattalin arziki. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Jami’ar Ofishin Jakadancin Canada A Shanghai Da Ta Bar Kasar

Next Post

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Related

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli
Daga Birnin Sin

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

3 hours ago
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

5 hours ago
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13
Daga Birnin Sin

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

6 hours ago
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka
Daga Birnin Sin

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

6 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

7 hours ago
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

9 hours ago
Next Post
Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.