ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin, Kyakkyawar Fata Ga Makomar Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Kasar Sin za ta jagoranci taro kai tsaye na farko cikin shekaru 31 tsakaninta da kasashen yankin tsakiyar Asiya da suka hada da Kazakhstan da Kyrgystan da Tajikistan da Turkmenistan da Uzbekistan, a ranakun 18 da 19 ga wata, wanda ke zaman muhimmin taro tsakanin bangarorin.

A ganina, wannan taro zai kara tabbatar da karfin kasar Sin na jagorantar kasashe masu tasowa wajen samun ci gaban da suke muradi da kuma ba su damar shiga ana damawa da su cikin harkokin kasa da kasa.

  • Karuwar Cinikin Wajen Sin A Watanni 4 Na Farkon Bana Ta Kai Kaso 5.8 Bisa Dari Kan Na Makamancin Lokaci Na Bara

Hakika ba al’ummar kasar Sin ne kadai ke amfana da ci gaban da kasar ta samu ba, har ma da kasashe masu tasowa, inda take fito da su tare da kara sanyawa ana jin amonsu, domin in ban da kasar Sin, babu wata babbar kasa dake kokarin jan kasashe masu tasowa a jiki da zuciya daya.

ADVERTISEMENT

Tarihi ya nuna cewa, kasar Sin na daya daga cikin kasashen da suka fara kulla huldar diflomasiyya da wadannan kasashe tun bayan samun ’yancin kansu, kuma tun daga lokacin ake samun kyautatuwar alaka a tsakaninsu.

Hakika hulda da kasar Sin babban tagomashi ne ga kowace kasa domin ta kasance mai tabbatar da adalci da aiwatar da dangantaka bisa girmama juna da moriyar juna, da kuma kaunar ganin an gudu tare an tsira tare. Burin kasar Sin a kullum shi ne ganin ci gaban kasashe masu tasowa, da burin ganin sun tsaya da kafarsu sun kuma nemi ci gaba ta hanyar da ta dace da su. Irin wannan ra’ayi shi ne ya dace da kyautata zaman lafiya da ci gaban duniya da ma kyautata zamantakewar al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Yayin da wasu kasashe suka dukufa wajen yin babakere da tsoma baki da neman ci da gumin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta kasance wata sabuwa kuma kyakkayawar fata ga makomar kasashe masu tasowa.

Bugu da kari, dangantakar wadannan kasashe za ta taimaka wajen kyautata zaman lafiyar yankin Asiya. Dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya, dangantaka ce ta moriyar juna bisa la’akari da hadin gwiwarsu a bangarori kamar na makamashi da fasaha da hakar ma’adinai da amfanin gona, inda kayayyakin wadannan bangarori da Sin ta shigo da su daga wadannan kasashe a bara, suka kasance mafi yawa, haka kuma su ne suka fi sayen kayayyakin laturoni da injuna daga kasar Sin.

Lamarin da ke nuna cewa, taron dake karatowa, zai kara bunkasa kyakkyawar dangantakar dake akwai tsakaninsu, tare da samar da karin sabbin damarmaki da ci gaban tattalin arziki. (Fa’iza Mustapha)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

Mutum 15 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.