• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila

by Bashir Bello, Abuja
2 years ago
in Siyasa
0
Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zababben Sanata mai wakiltar shiyyar Kano ta Kudu a Majalisar Dattawa, Sulaiman Abdulrahman Kawu Sumaila, ya bayyana cewa ‘yan majalisar tarayya ba za su lamunci duk wani shirin dauki-dora na shugabanni da jam’iyyar APC mai mulki ke shirin yi musu a zauren majalisar ba.

Kawu Sumaila, wanda ya kasance dan jam’iyyar adawa ta NNPP a zauren majalisar, ya bayyana hakan ne a wata tattaunawarsa da manema labarai a Abuja.

  • Matsalar Ruwan Sha: Yara 9 Sun Mutu A Kwale-Kwale, 12 Sun Bace A Zamfara
  • Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

A cewarsa, sun fara ganin jam’iyya mai mulki ta bayyana cewa ta ware wata shiyya da sunan neman mika mata ragamar shugabancin zauren majalisar a karo na 10, wanda shi ne abinnda suka fara gani a dimokuradiyya, amma su da suke da jinin wannan majalisar, ba za su taba bari wannan abu ya faru ba.

Sanatan, ya kara da cewa dole ne sai sun ce a’a game da wannan al’amarin domin kada tarihi ya zo a ci gaba da yin irin hakan, kuma za su tsaya tsayin-daka wajen ganin sun tabbatar da wannan abu bai yiwu ba, idan Allah Ya so ya yarda.

Ya ce, “Wannan al’amarin shi ne ya sake nuna cewa mun sake dawowa mulki irin na danniya na soja, amma idan salon mulki irin na dimokuradiyya muke koyi, to, muna da bangarori guda uku, wanda su ne na zartarwa, na majalisa dana shari’a wanda kowane gashin kansa yake ci.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

“Amma idan za a yi irin wannan magana, sai kowane ya je ya yi a bangarensa, amma bawai bangaren zartarwa su shiga cikin bangaren majalisa ba ko wani bangare ya yi kutse a cikin lamarin wani bangare ba.

“Hikima na yin irin wannan a kan duk wani shugaba mai cikakken iko shi ne, domin a samar da wani gurbi wanda za a rika tankwashe kafar shugaban kasa idan ya mike, to amma idan aka ce shi shugaban kasar ne da kan shi zai nada ma zauren shugabanni, to ba za a samu irin biyan bukatun da ake bukata ba.

“Sannan duk mun taho da bukatun mu iri daban-daban, kana ga irin abubuwan da suke ta faruwa a Nijeriya wanda mutane ke bukatar a sauya musu fasalin kasar ko a duba yanayin tsarin mulkin baki daya domin a gyara shi, ko kuma a yi cikakken tsari domin kowace juha ta rika rike kudinta da kanta, to abu mafi sauki ga mutanen da suka zo da irin wannan tunanin shi ne a bar su s uzo su zauna a karkashin zaure daya domin yan Nijeriya za su fi yarda da su.

Kawu Sumaila ya ci gaba da cewa, APC ba ita ba ce Nijeriya a bisa wasu dalilai guda biyu, inda ya bayyana cewa na daya ita ce, a cikin wannan majalisar ta 10, jam’iyyar APC tana da kashi 50 na ‘yan majalisa 59 daga cikin 109, yayin da sauran ‘yan adawa suna da kashi 55.

“Haka zalika a cikin daya zauren majalisar, jam’iyyar APC ba ta da rinjaye a ciki domin ‘yan adawa sun fi yawa.

“Abu na biyu shi ne, akalla mutane miliyan 90 da wani abu ne suka yi rajistar zabe a kasar nan, mutane miliyan 80 da wani abu ne suka karbi katin zabensu, amma karshe mutane miliyan 23 da wani abu ne suka je suka yi zabe, sannan a cikin mutum miliyan 23 da suka kada kuri’a, APC tana da miliyan takwas ne kacal, yayin da sauran jam’iyyun suna da sauran kuri’un.

“Wato hakan ke nuna cewa ‘yan Nijeriya sun bar ‘yan siyasa ne da halinsu domin ba su yarda da su ba saboda gani suke yi kowa irin jiya ne idan an dawo kuma wannan shi ne lokacin da ya kamata a ce an samar da gyara sama da kowane lokaci domin wanda ya zama shugaban kasa a APC, mutum ne wanda ya yi gwagwarmayar tabbatar da dimokuradiyya a kasar nan.

“Har ila yau, sabon zababben shugaban kasar, mutum ne da ya jagorance mu a zama daban-daban kuma ya koya mana na ki har ya shiga jikinmu ta yadda duk mutumin da ya zo ya ce mana a’a, sai mu ce masa na ki don shi ya koya mana na ki.

“Yanzu ba zancen fada ko tashin hankali ba ne, illa ranar zaben shugabannin majalisar kawai za a shiga zaurorin nan a je a yi zabe domin a zabi wanda ake so saboda kowa ya cancanta kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar nan ya fada tare da na dokokin majalisar.” in ji shi

A karshe, Sanatan, ya nuna cewa za su zabi wanda suke so, kuma kowa ya san gaskiya ba wai ‘yan adawa kawai ba, kana sun tabbatar da cewa za a zabi sabbin shugabanni kuma za su fito ne daga cikin jam’iyyar APC mai Mulki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dauki-DoraKawu SumailamajalisaShugabannin Majalisa Ta 10TinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalar Ruwan Sha: Yara 9 Sun Mutu A Kwale-Kwale, 12 Sun Bace A Zamfara

Next Post

Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?

Related

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 day ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

2 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

5 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

5 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

1 week ago
Next Post
Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?

Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?

LABARAI MASU NASABA

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

September 11, 2025
Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

September 11, 2025
Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

September 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

September 11, 2025
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.