ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
Kawu Sumaila

Zababben Sanata mai wakiltar shiyyar Kano ta Kudu a Majalisar Dattawa, Sulaiman Abdulrahman Kawu Sumaila, ya bayyana cewa ‘yan majalisar tarayya ba za su lamunci duk wani shirin dauki-dora na shugabanni da jam’iyyar APC mai mulki ke shirin yi musu a zauren majalisar ba.

Kawu Sumaila, wanda ya kasance dan jam’iyyar adawa ta NNPP a zauren majalisar, ya bayyana hakan ne a wata tattaunawarsa da manema labarai a Abuja.

  • Matsalar Ruwan Sha: Yara 9 Sun Mutu A Kwale-Kwale, 12 Sun Bace A Zamfara
  • Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

A cewarsa, sun fara ganin jam’iyya mai mulki ta bayyana cewa ta ware wata shiyya da sunan neman mika mata ragamar shugabancin zauren majalisar a karo na 10, wanda shi ne abinnda suka fara gani a dimokuradiyya, amma su da suke da jinin wannan majalisar, ba za su taba bari wannan abu ya faru ba.

ADVERTISEMENT

Sanatan, ya kara da cewa dole ne sai sun ce a’a game da wannan al’amarin domin kada tarihi ya zo a ci gaba da yin irin hakan, kuma za su tsaya tsayin-daka wajen ganin sun tabbatar da wannan abu bai yiwu ba, idan Allah Ya so ya yarda.

Ya ce, “Wannan al’amarin shi ne ya sake nuna cewa mun sake dawowa mulki irin na danniya na soja, amma idan salon mulki irin na dimokuradiyya muke koyi, to, muna da bangarori guda uku, wanda su ne na zartarwa, na majalisa dana shari’a wanda kowane gashin kansa yake ci.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

“Amma idan za a yi irin wannan magana, sai kowane ya je ya yi a bangarensa, amma bawai bangaren zartarwa su shiga cikin bangaren majalisa ba ko wani bangare ya yi kutse a cikin lamarin wani bangare ba.

“Hikima na yin irin wannan a kan duk wani shugaba mai cikakken iko shi ne, domin a samar da wani gurbi wanda za a rika tankwashe kafar shugaban kasa idan ya mike, to amma idan aka ce shi shugaban kasar ne da kan shi zai nada ma zauren shugabanni, to ba za a samu irin biyan bukatun da ake bukata ba.

“Sannan duk mun taho da bukatun mu iri daban-daban, kana ga irin abubuwan da suke ta faruwa a Nijeriya wanda mutane ke bukatar a sauya musu fasalin kasar ko a duba yanayin tsarin mulkin baki daya domin a gyara shi, ko kuma a yi cikakken tsari domin kowace juha ta rika rike kudinta da kanta, to abu mafi sauki ga mutanen da suka zo da irin wannan tunanin shi ne a bar su s uzo su zauna a karkashin zaure daya domin yan Nijeriya za su fi yarda da su.

Kawu Sumaila ya ci gaba da cewa, APC ba ita ba ce Nijeriya a bisa wasu dalilai guda biyu, inda ya bayyana cewa na daya ita ce, a cikin wannan majalisar ta 10, jam’iyyar APC tana da kashi 50 na ‘yan majalisa 59 daga cikin 109, yayin da sauran ‘yan adawa suna da kashi 55.

“Haka zalika a cikin daya zauren majalisar, jam’iyyar APC ba ta da rinjaye a ciki domin ‘yan adawa sun fi yawa.

“Abu na biyu shi ne, akalla mutane miliyan 90 da wani abu ne suka yi rajistar zabe a kasar nan, mutane miliyan 80 da wani abu ne suka karbi katin zabensu, amma karshe mutane miliyan 23 da wani abu ne suka je suka yi zabe, sannan a cikin mutum miliyan 23 da suka kada kuri’a, APC tana da miliyan takwas ne kacal, yayin da sauran jam’iyyun suna da sauran kuri’un.

“Wato hakan ke nuna cewa ‘yan Nijeriya sun bar ‘yan siyasa ne da halinsu domin ba su yarda da su ba saboda gani suke yi kowa irin jiya ne idan an dawo kuma wannan shi ne lokacin da ya kamata a ce an samar da gyara sama da kowane lokaci domin wanda ya zama shugaban kasa a APC, mutum ne wanda ya yi gwagwarmayar tabbatar da dimokuradiyya a kasar nan.

“Har ila yau, sabon zababben shugaban kasar, mutum ne da ya jagorance mu a zama daban-daban kuma ya koya mana na ki har ya shiga jikinmu ta yadda duk mutumin da ya zo ya ce mana a’a, sai mu ce masa na ki don shi ya koya mana na ki.

“Yanzu ba zancen fada ko tashin hankali ba ne, illa ranar zaben shugabannin majalisar kawai za a shiga zaurorin nan a je a yi zabe domin a zabi wanda ake so saboda kowa ya cancanta kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar nan ya fada tare da na dokokin majalisar.” in ji shi

A karshe, Sanatan, ya nuna cewa za su zabi wanda suke so, kuma kowa ya san gaskiya ba wai ‘yan adawa kawai ba, kana sun tabbatar da cewa za a zabi sabbin shugabanni kuma za su fito ne daga cikin jam’iyyar APC mai Mulki.

Kawu Sumaila
Bashir Bello, Abuja
+ postsBio
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    APC Ce Za Ta Yi Nasarar Samar Da Shugabanci A Majalisa – Hon. Wase
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Shugabancin Majalisa: Na Fi Kowa Cancanta, Ni Kadai Na Kawo Kudiri 78, Guda 21 Shugaban Kasa Ya Sa Wa Hannu – Hon Abbas Tajudeen

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?

Shugabancin Majalisa Ta 10: Ko ‘Yan Mowar APC Za Su Kai Bantensu?

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.