• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Dauki Sabbin Ma’aikata 1,683

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Dauki Sabbin Ma’aikata 1,683
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad ya fara wa’adin mulkinsa na biyu da daukar sabbin ma’aikata 1,684 a bangarori daban-daban na aikin gwamnati.

Hakan na kunshe ne cikin manufar shawo kan karancin ma’aikatan da ake fuskanta a wasu ma’aikatu, fannoni da rassan gwamnati.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Nada Masu Bashi Shawara 20
  • Kotu Ta Dakatar Da EFCC, ICPC, DSS Daga Tsare Sanata Yari

Da yake zantawa da ‘yan jarida kan wannan lamarin, shugaban ma’aikatan jihar Bauchi, Alhaji Yahuza Adamu Haruna, ya shaida cewar, daga cikin ma’aikatan, sama da mutum dubu daya an dauke su ne a bangaren koyar da ilimi domin shawo kan matsalar da ake fuskanta a harkar ilimi a jihar.

Ya ce, malaman da aka dauka sun kunshi har da masu kuyar da muhimman darussa da suka hada da na turanci, lissafi, biology, Biology, Chemistry, Physics da kuma na ICT. Dukka a bangaren ilimin, ya kuma sanar da cewa, gwamnan ya kuma amince da daukan wasu karin malamai guda 154 da za su yi aiki a kwalejin koyar da ilimi ta Aminu Saleh da ke Azare.

Idan za ku tuna dai, a jawabinsa na shan rantsuwar kama aiki a matsayin gwamnan jihar Bauchi karo na biyu, Bala Muhammad ya shaida cewar, jihar ta cire takunkumin daukan ma’aikata domin bai wa matasan da suka dace cikakken damar shigowa a dama da su wajen tafiyar da aikin gwamnati, kan hakan ne ya nuna cewa kwanan nan za a fara daukan sabbin ma’aikata.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Yahuza ya ce, gwamnati mai ci a jihar ta Bala Muhammad ta himmatu wajen tabbatar da aiki mai inganci domin kyautata rayuwar al’umma da cigaban Jihar Bauchi.

Ya ce, “Sannu a hankali gwamna Bala Muhammad ya amince da fara daukan ma’aikata, inda ya amince da daukan ma’aikata dubu daya a ma’aikatar ilimi sannan ya amince da daukan wasu ma’aikatan a fannoni daban-daban.

“A bangaren harkar noma ma, gwamnan ya amince da daukan ma’aikatan domin magance matsalar da ake fama da shi na karancin malaman gona.”

“Tun lokacin da gwamnan ya yi alkawari a wajen jawabinsa na rantsuwa, ga shi ba da jimawa ba har ya amince da daukan ma’aikatan, kuma nan ba da jimawa ba ma zai sake daukan wasu. Wannan abun yabawa ne matuka da masa jinjina.”

Daga nan sai ya gargadi masu bukatar aiki da cewa su sanya lura kada wani ko wasu su zo musu da cewa su basu wani abu domin samar musu da aikin yi, “Don Allah a taimakemu duk wanda ya ce a ba shi sisi don ya samar ma wani da aikin yi, to a yi gaggawar zuwa domin samar mana, mu kuma za mu dauki mataki kan kowaye,” ya shaida.

Shugaban ma’aikatan ya bada jerin sabbin ma’aikatan da gwamnan ya dauka da cewa ma’aikatar ilimi ta samu sabbin ma’aikata 1,000; ma’aikatar aikin gona 44; ma’aikatar bunkasa aikin gona (BSADP) 206; ma’aikatar samar da kayan noma da rarrabashi (BASADA) ta samu sabbin jami’ai 90; sai ma’aikatar mata da cigaban yara mai sabbin ma’aikata 70; kwalejin ilimi ta Aminu Saleh, Azare 154; sai kuma kotun daukaka kara ta Shari’a mai sabbin ma’aikata 120.

Daga bisani ya nemi sabbun ma’aikatan da su hada kai da gwamnatin jihar domin ciyar da aiki da jihar Bauchi gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bala MohammedBauchiSabbin Ma'aikata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Ana Kokarin Yaki Da Yaduwar Hamada A Sin Don Bude Sabon Babi

Next Post

Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

48 minutes ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

1 hour ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

4 hours ago
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

7 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

8 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

10 hours ago
Next Post
Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.