• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Dauki Sabbin Ma’aikata 1,683

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Dauki Sabbin Ma’aikata 1,683
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad ya fara wa’adin mulkinsa na biyu da daukar sabbin ma’aikata 1,684 a bangarori daban-daban na aikin gwamnati.

Hakan na kunshe ne cikin manufar shawo kan karancin ma’aikatan da ake fuskanta a wasu ma’aikatu, fannoni da rassan gwamnati.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Nada Masu Bashi Shawara 20
  • Kotu Ta Dakatar Da EFCC, ICPC, DSS Daga Tsare Sanata Yari

Da yake zantawa da ‘yan jarida kan wannan lamarin, shugaban ma’aikatan jihar Bauchi, Alhaji Yahuza Adamu Haruna, ya shaida cewar, daga cikin ma’aikatan, sama da mutum dubu daya an dauke su ne a bangaren koyar da ilimi domin shawo kan matsalar da ake fuskanta a harkar ilimi a jihar.

Ya ce, malaman da aka dauka sun kunshi har da masu kuyar da muhimman darussa da suka hada da na turanci, lissafi, biology, Biology, Chemistry, Physics da kuma na ICT. Dukka a bangaren ilimin, ya kuma sanar da cewa, gwamnan ya kuma amince da daukan wasu karin malamai guda 154 da za su yi aiki a kwalejin koyar da ilimi ta Aminu Saleh da ke Azare.

Idan za ku tuna dai, a jawabinsa na shan rantsuwar kama aiki a matsayin gwamnan jihar Bauchi karo na biyu, Bala Muhammad ya shaida cewar, jihar ta cire takunkumin daukan ma’aikata domin bai wa matasan da suka dace cikakken damar shigowa a dama da su wajen tafiyar da aikin gwamnati, kan hakan ne ya nuna cewa kwanan nan za a fara daukan sabbin ma’aikata.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Yahuza ya ce, gwamnati mai ci a jihar ta Bala Muhammad ta himmatu wajen tabbatar da aiki mai inganci domin kyautata rayuwar al’umma da cigaban Jihar Bauchi.

Ya ce, “Sannu a hankali gwamna Bala Muhammad ya amince da fara daukan ma’aikata, inda ya amince da daukan ma’aikata dubu daya a ma’aikatar ilimi sannan ya amince da daukan wasu ma’aikatan a fannoni daban-daban.

“A bangaren harkar noma ma, gwamnan ya amince da daukan ma’aikatan domin magance matsalar da ake fama da shi na karancin malaman gona.”

“Tun lokacin da gwamnan ya yi alkawari a wajen jawabinsa na rantsuwa, ga shi ba da jimawa ba har ya amince da daukan ma’aikatan, kuma nan ba da jimawa ba ma zai sake daukan wasu. Wannan abun yabawa ne matuka da masa jinjina.”

Daga nan sai ya gargadi masu bukatar aiki da cewa su sanya lura kada wani ko wasu su zo musu da cewa su basu wani abu domin samar musu da aikin yi, “Don Allah a taimakemu duk wanda ya ce a ba shi sisi don ya samar ma wani da aikin yi, to a yi gaggawar zuwa domin samar mana, mu kuma za mu dauki mataki kan kowaye,” ya shaida.

Shugaban ma’aikatan ya bada jerin sabbin ma’aikatan da gwamnan ya dauka da cewa ma’aikatar ilimi ta samu sabbin ma’aikata 1,000; ma’aikatar aikin gona 44; ma’aikatar bunkasa aikin gona (BSADP) 206; ma’aikatar samar da kayan noma da rarrabashi (BASADA) ta samu sabbin jami’ai 90; sai ma’aikatar mata da cigaban yara mai sabbin ma’aikata 70; kwalejin ilimi ta Aminu Saleh, Azare 154; sai kuma kotun daukaka kara ta Shari’a mai sabbin ma’aikata 120.

Daga bisani ya nemi sabbun ma’aikatan da su hada kai da gwamnatin jihar domin ciyar da aiki da jihar Bauchi gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bala MohammedBauchiSabbin Ma'aikata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Ana Kokarin Yaki Da Yaduwar Hamada A Sin Don Bude Sabon Babi

Next Post

Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Next Post
Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.