ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Dauki Sabbin Ma’aikata 1,683

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad ya fara wa’adin mulkinsa na biyu da daukar sabbin ma’aikata 1,684 a bangarori daban-daban na aikin gwamnati.

Hakan na kunshe ne cikin manufar shawo kan karancin ma’aikatan da ake fuskanta a wasu ma’aikatu, fannoni da rassan gwamnati.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Nada Masu Bashi Shawara 20
  • Kotu Ta Dakatar Da EFCC, ICPC, DSS Daga Tsare Sanata Yari

Da yake zantawa da ‘yan jarida kan wannan lamarin, shugaban ma’aikatan jihar Bauchi, Alhaji Yahuza Adamu Haruna, ya shaida cewar, daga cikin ma’aikatan, sama da mutum dubu daya an dauke su ne a bangaren koyar da ilimi domin shawo kan matsalar da ake fuskanta a harkar ilimi a jihar.

ADVERTISEMENT

Ya ce, malaman da aka dauka sun kunshi har da masu kuyar da muhimman darussa da suka hada da na turanci, lissafi, biology, Biology, Chemistry, Physics da kuma na ICT. Dukka a bangaren ilimin, ya kuma sanar da cewa, gwamnan ya kuma amince da daukan wasu karin malamai guda 154 da za su yi aiki a kwalejin koyar da ilimi ta Aminu Saleh da ke Azare.

Idan za ku tuna dai, a jawabinsa na shan rantsuwar kama aiki a matsayin gwamnan jihar Bauchi karo na biyu, Bala Muhammad ya shaida cewar, jihar ta cire takunkumin daukan ma’aikata domin bai wa matasan da suka dace cikakken damar shigowa a dama da su wajen tafiyar da aikin gwamnati, kan hakan ne ya nuna cewa kwanan nan za a fara daukan sabbin ma’aikata.

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yahuza ya ce, gwamnati mai ci a jihar ta Bala Muhammad ta himmatu wajen tabbatar da aiki mai inganci domin kyautata rayuwar al’umma da cigaban Jihar Bauchi.

Ya ce, “Sannu a hankali gwamna Bala Muhammad ya amince da fara daukan ma’aikata, inda ya amince da daukan ma’aikata dubu daya a ma’aikatar ilimi sannan ya amince da daukan wasu ma’aikatan a fannoni daban-daban.

“A bangaren harkar noma ma, gwamnan ya amince da daukan ma’aikatan domin magance matsalar da ake fama da shi na karancin malaman gona.”

“Tun lokacin da gwamnan ya yi alkawari a wajen jawabinsa na rantsuwa, ga shi ba da jimawa ba har ya amince da daukan ma’aikatan, kuma nan ba da jimawa ba ma zai sake daukan wasu. Wannan abun yabawa ne matuka da masa jinjina.”

Daga nan sai ya gargadi masu bukatar aiki da cewa su sanya lura kada wani ko wasu su zo musu da cewa su basu wani abu domin samar musu da aikin yi, “Don Allah a taimakemu duk wanda ya ce a ba shi sisi don ya samar ma wani da aikin yi, to a yi gaggawar zuwa domin samar mana, mu kuma za mu dauki mataki kan kowaye,” ya shaida.

Shugaban ma’aikatan ya bada jerin sabbin ma’aikatan da gwamnan ya dauka da cewa ma’aikatar ilimi ta samu sabbin ma’aikata 1,000; ma’aikatar aikin gona 44; ma’aikatar bunkasa aikin gona (BSADP) 206; ma’aikatar samar da kayan noma da rarrabashi (BASADA) ta samu sabbin jami’ai 90; sai ma’aikatar mata da cigaban yara mai sabbin ma’aikata 70; kwalejin ilimi ta Aminu Saleh, Azare 154; sai kuma kotun daukaka kara ta Shari’a mai sabbin ma’aikata 120.

Daga bisani ya nemi sabbun ma’aikatan da su hada kai da gwamnatin jihar domin ciyar da aiki da jihar Bauchi gaba.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

Qin Gang Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministan Harkokin Wajen Afirka Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.