• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Sin Da Amurka Su Gina Alaka Da Juna Karkashin Salon Martaba Juna Da Daidaito

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Zama Wajibi Sin Da Amurka Su Gina Alaka Da Juna Karkashin Salon Martaba Juna Da Daidaito
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya ce ya zama wajibi kasashen Sin da Amurka su gina alaka bisa salon martaba juna da daidaito, da girmama bambance-bambancensu na tarihi, da al’adu, da tsarin zamantakewa da hanyoyin ci gaba. Kaza lika ya wajaba sassan biyu su kare moriya, da manyan abubuwan da ke jan hankalin su.

Wang Wenbin, wanda ya bayyana hakan a Juma’ar nan, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, ya ce wasu rahotanni sun ruwaito cewa, a ranar Laraba, fadar White House ta Amurka ta shaidawa manema labarai shirin sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken, na ziyartar kasar Sin, inda aka bayyana cewa, Amurka na aiwatar da manufofin cudanya da kasar Sin masu dorewa, wato salon dangantakar sassan biyu yana kunshe da takara ba wai neman tashin hankali, fito-na-fito, ko sabon salon cacar baka ba.

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Gimama Mabambantan Wayewar Kai Ta Bil Adama

Kaza lika Amurka na fatan ci gaba da gudanar da takara mai tsafta. Za ta kuma yi kokarin daidaita yanayin takara tare da Sin, da kuma bunkasa hadin gwiwa kan batutuwan da suka dace da burikan su.

Da yake amsa tambayar da aka yi masa kan wannan batu, Wang Wenbin ya ce shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sha nanata cewa, bai dace alakar Sin da Amurka ta zama ta idan bangare daya ya samu dayan ya yi asara ba, maimakon haka, dacewa ya yi sassan biyu su rika cimma nasara tare, ta yadda kowa zai iya samun riba ko hasara.

Ya ce ya kamata Sin da Amurka su rika kallon juna a matsayin abokan tafiya, a manufofin su na gida da na waje, da aiwatar da manyan tsare-tsare bisa ka’idoji, da nacewa martaba juna, da tafiya tare, bisa zaman lafiya da hadin gwiwar cimma moriyar juna. Kana su lalubo hanya mafi dacewa ta kyautata jituwa tsakanin su. Hakan ne zai kare moriyar su, da ma irin fata da sassan kasa da kasa ke yi musu.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

A wani ci gaban kuma, kamfanin tsaron yanar gizo na Amurka mai suna “Mandiant Corporation”, ya fitar da wata sanarwa a baya-bayan nan, wadda a cikin ta ya ce, yana zargin kasar Sin da baiwa wasu masu kutsen yanar gizo goyon baya, inda suka yi kutse cikin daruruwan na’urori masu kwakwalwa na gwamnati, da na sassa masu zaman kan su dake kasashe daban daban.

Da yake amsa tambaya game da hakan, Wang Wenbin ya ce da ma wannan kamfani ya sha fitar da irin wadannan rahotanni na karya, game da wadanda yake kira da wai “masu kutsen yanar gizo na Sin”, kuma abubuwan dake kunshe cikin rahoton kamfanin ba kamshin gaskiya ko kwarewar aiki a cikin su. (Saminu Alhassan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Dakatar Da Godwin Emefiele Zai Farfado Da Tattalin Arzikin Kasa?

Next Post

Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar ‘Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

7 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

7 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

8 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

10 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

11 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

13 hours ago
Next Post
Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar ‘Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar 'Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.