ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Sin Da Amurka Su Gina Alaka Da Juna Karkashin Salon Martaba Juna Da Daidaito

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya ce ya zama wajibi kasashen Sin da Amurka su gina alaka bisa salon martaba juna da daidaito, da girmama bambance-bambancensu na tarihi, da al’adu, da tsarin zamantakewa da hanyoyin ci gaba. Kaza lika ya wajaba sassan biyu su kare moriya, da manyan abubuwan da ke jan hankalin su.

Wang Wenbin, wanda ya bayyana hakan a Juma’ar nan, yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa, ya ce wasu rahotanni sun ruwaito cewa, a ranar Laraba, fadar White House ta Amurka ta shaidawa manema labarai shirin sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken, na ziyartar kasar Sin, inda aka bayyana cewa, Amurka na aiwatar da manufofin cudanya da kasar Sin masu dorewa, wato salon dangantakar sassan biyu yana kunshe da takara ba wai neman tashin hankali, fito-na-fito, ko sabon salon cacar baka ba.

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Gimama Mabambantan Wayewar Kai Ta Bil Adama

Kaza lika Amurka na fatan ci gaba da gudanar da takara mai tsafta. Za ta kuma yi kokarin daidaita yanayin takara tare da Sin, da kuma bunkasa hadin gwiwa kan batutuwan da suka dace da burikan su.

ADVERTISEMENT

Da yake amsa tambayar da aka yi masa kan wannan batu, Wang Wenbin ya ce shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sha nanata cewa, bai dace alakar Sin da Amurka ta zama ta idan bangare daya ya samu dayan ya yi asara ba, maimakon haka, dacewa ya yi sassan biyu su rika cimma nasara tare, ta yadda kowa zai iya samun riba ko hasara.

Ya ce ya kamata Sin da Amurka su rika kallon juna a matsayin abokan tafiya, a manufofin su na gida da na waje, da aiwatar da manyan tsare-tsare bisa ka’idoji, da nacewa martaba juna, da tafiya tare, bisa zaman lafiya da hadin gwiwar cimma moriyar juna. Kana su lalubo hanya mafi dacewa ta kyautata jituwa tsakanin su. Hakan ne zai kare moriyar su, da ma irin fata da sassan kasa da kasa ke yi musu.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

A wani ci gaban kuma, kamfanin tsaron yanar gizo na Amurka mai suna “Mandiant Corporation”, ya fitar da wata sanarwa a baya-bayan nan, wadda a cikin ta ya ce, yana zargin kasar Sin da baiwa wasu masu kutsen yanar gizo goyon baya, inda suka yi kutse cikin daruruwan na’urori masu kwakwalwa na gwamnati, da na sassa masu zaman kan su dake kasashe daban daban.

Da yake amsa tambaya game da hakan, Wang Wenbin ya ce da ma wannan kamfani ya sha fitar da irin wadannan rahotanni na karya, game da wadanda yake kira da wai “masu kutsen yanar gizo na Sin”, kuma abubuwan dake kunshe cikin rahoton kamfanin ba kamshin gaskiya ko kwarewar aiki a cikin su. (Saminu Alhassan)

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar ‘Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

Kokarin Tinubu Wajen Inganta Rayuwar 'Yan Nijeriya Bayan Cire Tallafin Mai

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.